< Genèse 18 >
1 Or le Seigneur apparut dans la vallée de Mambré, à Abraham, assis à l’entrée de sa tente dans la grande chaleur du jour.
Ubangiji ya bayyana ga Ibrahim kusa da manyan itatuwan Mamre yayinda yake zaune a mashigin tentinsa da tsakar rana.
2 Car, lorsqu’il eut levé les yeux, trois hommes lui apparurent se tenant près de lui; et lorsqu’il les eut vus, il courut au-devant d’eux de l’entrée de sa tente, et il se prosterna en terre.
Da Ibrahim ya ɗaga ido, sai ya ga mutum uku suna tsaye kusa da shi. Sa’ad da ya gan su, sai ya tashi nan da nan daga mashigin tentinsa, ya tarye su, ya rusuna har ƙasa.
3 Et il dit: Seigneur, si j’ai trouvé grâce à tes yeux, ne passe pas au-delà de ton serviteur.
Ya ce, “Ranka yă daɗe, in na sami tagomashi daga gare ku kada ku wuce bawanku.
4 J’apporterai un peu d’eau, et vous laverez vos pieds, et vous vous reposerez sous cet arbre.
Bari a kawo ruwa ku wanke ƙafafunku, ku huta a ƙarƙashin wannan itace.
5 Je vous servirai aussi un peu de pain; et vous reprendrez vos forces, puis vous irez plus loin, car c’est pour cela que vous êtes venus vers votre serviteur. Ils lui répondirent: Fais ce que tu as dit.
Bari in samo muku wani abu ku ci don ku wartsake, sa’an nan ku ci gaba da tafiyarku; da yake kun biyo wurin bawanku.” Suka ce, “To, sai ka yi abin da ka ce.”
6 Et Abraham alla en toute hâte à sa tente vers Sara, et lui dit: Pétris vite trois mesures de fleur de farine, et fais des pains cuits sous la cendre.
Saboda haka Ibrahim ya ruga zuwa wurin Saratu a cikin tenti ya ce, “Yi sauri, ki shirya mudu uku na gari mai laushi, ki cuɗa shi, ki yi burodi.”
7 Et lui-même courut au troupeau, et en prit un veau tendre et excellent; et il le donna à un serviteur qui se hâta et le fit cuire.
Sa’an nan Ibrahim ya yi gudu zuwa garkensa, ya zaɓi ɗan maraƙi ya ba wa bawansa, bawansa kuma ya yi sauri ya gyara shi.
8 Il prit aussi du beurre et du lait, et le veau qu’il avait fait cuire, et le mit devant eux; et lui-même se tenait debout près d’eux sous l’arbre.
Sa’an nan Ibrahim ya ɗauko dambu da madara da naman ɗan maraƙin da aka gyara, ya kawo a gabansu. Yayinda suke ci, ya tsaya a gindin itace kusa da su.
9 Quand ils eurent mangé, ils lui demandèrent: Où est Sara ta femme? Il répondit: La voilà dans la tente.
Sai suka ce masa, “Ina Saratu matarka?” Ibrahim ya ce, “Tana can cikin tenti.”
10 L’un d’eux dit: En retournant, je viendrai vers toi en ce temps-ci, vous vivant encore, et Sara ta femme aura un fils. Ce qu’ayant entendu, Sara rit derrière la porte de la tente.
Sa’an nan ɗayansu ya ce, “Lalle zan komo wurinka war haka shekara mai zuwa. Saratu matarka kuwa za tă haifi ɗa.” Saratu kuwa tana a bayansu tana ji daga mashigin tenti.
11 Car ils étaient tous deux vieux et d’un âge fort avancé, et Sara n’avait plus ses mois.
Ibrahim da Saratu dai sun riga sun tsufa sosai. Saratu kuma ta wuce shekarun haihuwa.
12 Elle rit en cachette, disant: Après que je suis devenue vieille, et que mon seigneur est un peu bien vieux, penserai-je au plaisir?
Saboda haka Saratu ta yi dariya da ta yi tunani a zuci tana cewa, “Bayan ƙarfina ya ƙare, maigidana kuma ya tsufa, yanzu zan sami wannan jin daɗi?”
13 Mais le Seigneur dit à Abraham: Pourquoi Sara a-t-elle ri, disant: Est-ce que vraiment je dois enfanter, moi vieille?
Sai Ubangiji ya ce wa Ibrahim, “Me ya ba Saratu dariya har da ta ce, ‘Har zan iya haifi ɗa duk ta tsufata yanzu?’
14 Est-ce qu’à Dieu quelque chose est difficile? Selon ma parole, je reviendrai vers toi, en ce même temps, vous vivant encore, et Sara aura un fils.
Akwai abin zai gagari Ubangiji? Zan komo wurinka a ƙayyadadden lokacin nan shekara mai zuwa kuma Saratu za tă haifi ɗa.”
15 Sara le nia, disant: Je n’ai pas ri; car elle était saisie de crainte. Mais le Seigneur: Il n’en est pas ainsi, dit-il; mais tu as ri.
Saratu ta ji tsoro, don haka sai ta yi ƙarya ta ce, “Ban yi dariya ba.” Ya ce, “A’a, kin yi dariya.”
16 Lors donc que ces hommes furent partis de là, ils tournèrent les yeux vers Sodome; et Abraham allait avec eux, les reconduisant.
Sai mutanen suka tashi suka nufi Sodom, Ibrahim kuwa ya yi musu rakiya, ya yi bankwana da su.
17 Alors le Seigneur dit: Pourrai-je cacher à Abraham ce que je vais faire,
Sai Ubangiji ya ce, “Zan ɓoye wa Ibrahim abin da nake shirin yi?
18 Puisqu’il doit être père d’une nation grande et très puissante, et que doivent être bénies en lui toutes les nations de la terre?
Lalle Ibrahim zai zama al’umma mai girma da kuma mai iko, kuma ta wurinsa dukan al’umman duniya za su sami albarka.
19 Car je sais qu’il ordonnera à ses enfants et à sa maison après lui, de garder la voie du Seigneur, et de pratiquer l’équité et la justice, afin que le Seigneur accomplisse à cause d’Abraham tout ce qu’il lui a dit.
Saboda na zaɓe shi don yă umarci’ya’yansa da iyalinsa a bayansa su kiyaye hanyoyin Ubangiji, ta wurin yin abin da yake daidai da kuma yin adalci, domin Ubangiji ya aikata abin da ya yi wa Ibrahim alkawari.”
20 Le Seigneur dit donc: La clameur de Sodome et de Gomorrhe s’est multipliée, et leur péché s’est agravé outre mesure,
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kuka a kan Sodom da Gomorra ta yi yawa, zunubinsu kuma ya yi muni sosai,
21 Je descendrai, et je verrai, si la clameur qui est venue jusqu’à moi, elles l’ont accomplie par leurs œuvres: s’il n’en est pas ainsi, que je le sache.
zan gangara in ga ko abin da suka yi ya yi muni kamar yadda kukan ya zo gare ni, zan bincike.”
22 Et ils partirent de là, et ils s’en allèrent vers Sodome; mais Abraham se tenait encore devant le Seigneur.
Sai mutanen suka juya suka nufi wajen Sodom amma Ibrahim ya ci gaba da kasance a gaban Ubangiji.
23 Et s’approchant, il dit: Est-ce que vous perdrez le juste avec l’impie?
Sai Ibrahim ya matso wurinsa ya ce, “Za ka hallaka masu adalci tare da masu mugunta?
24 S’il se trouve cinquante justes dans la ville, périront-ils avec les autres? et ne pardonnerez-vous pas à ce lieu à cause de ces cinquante justes, s’ils s’y trouvent?
Me zai faru in akwai mutum hamshin masu adalci a cikin birnin? Ashe, za ka hallaka shi, ba za ka cece wurin saboda mutane hamsin nan masu adalcin da suke a cikinsa ba?
25 Loin de vous de faire cela, de perdre le juste avec l’impie, en sorte que le juste soit traité comme l’impie; cela n’est pas de vous: vous qui jugez toute la terre, vous ne rendrez nullement ce jugement.
Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba, ka kashe masu adalci tare da masu mugunta, ka ɗauka masu adalci da masu mugunta daidai? Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba! Mai hukuncin dukan duniya ba zai aikata gaskiya ba?”
26 Le Seigneur lui répondit: Si je trouve à Sodome cinquante justes, dans l’enceinte de la ville, je pardonnerai à tout ce lieu à cause d’eux.
Ubangiji ce, “In na sami mutum hamshin masu adalci a cikin birnin Sodom, zan bar dukan birnin saboda su.”
27 Et reprenant. Abraham dit: Puisque j’ai déjà commencé, je parlerai à mon Seigneur, quoique je ne sois que poussière et cendre.
Sai Ibrahim ya ƙara cewa, “Yanzu da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, ko da yake ni ba kome ba ne illa turɓaya da toka,
28 Et s’il y avait cinquante justes, moins cinq, détruiriez-vous, parce qu’il n’y en aurait que quarante-cinq, la ville entière? Et le Seigneur dit: Je ne la détruirai pas, si j’en trouve là quarante-cinq.
in yawan masu adalci sun kāsa hamshin da mutum biyar fa? Za ka hallaka dukan birnin saboda rashin mutum biyar ɗin?” Ya ce, “In na sami mutum arba’in da biyar a wurin, ba zan hallaka shi ba.”
29 Et il lui parla de nouveau: Mais s’il s’en trouve là quarante, que ferez-vous? Dieu répondit: Je ne la frapperai pas, à cause des quarante.
Ya sāke cewa, “In mutum arba’in kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda mutum arba’in ɗin, ba zan aikata ba.”
30 Je vous prie, Seigneur, ajouta Abraham, ne vous fâchez point, si je parle encore: Et s’il s’en trouve là trente? Le Seigneur répondit: Je ne le ferai pas, si j’en trouve là trente.
Sai ya ce, “Kada Ubangiji ya yi fushi, amma bari in ƙara magana. A ce mutum talatin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Ba zan aikata ba, in na sami mutum talatin a can.”
31 Puisque j’ai déjà commencé, dit encore Abraham, je parlerai à mon Seigneur: Et s’il s’y en trouvait vingt? Le Seigneur répondit: Je ne la détruirai pas, à cause des vingt.
Ibrahim ya ce, “Yanzu fa da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, in ashirin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda ashirin ɗin, ba zan hallaka shi ba.”
32 Je vous conjure. Seigneur, reprit Abraham, ne vous irritez pas, si je parle encore une fois: Et s’il s’en trouve là dix? Et le Seigneur dit: Je ne la détruirai pas à cause des dix.
Sa’an nan Ibrahim ya ce, “Kada Ubangiji yă yi fushi, amma bari in ƙara magana sau ɗaya tak. In aka sami mutum goma kaɗai a can fa?” Ubangiji ya ce, “Saboda goma nan, ba zan hallaka shi ba.”
33 Et le Seigneur s’en alla, après qu’il eut cessé de parler à Abraham, et Abraham retourna en sa demeure.
Sa’ad da Ubangiji ya gama magana da Ibrahim, ya tafi, Ibrahim kuma ya koma gida.