< Psaumes 72 >
1 De Salomon. O Dieu, donne tes jugements au roi, Et ta justice au fils du roi!
Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
2 Il jugera ton peuple avec justice, Et tes malheureux avec équité.
Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
3 Les montagnes porteront la paix pour le peuple, Et les collines aussi, par l’effet de ta justice.
Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
4 Il fera droit aux malheureux du peuple, Il sauvera les enfants du pauvre, Et il écrasera l’oppresseur.
Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
5 On te craindra, tant que subsistera le soleil, Tant que paraîtra la lune, de génération en génération.
Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
6 Il sera comme une pluie qui tombe sur un terrain fauché, Comme des ondées qui arrosent la campagne.
Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
7 En ses jours le juste fleurira, Et la paix sera grande jusqu’à ce qu’il n’y ait plus de lune.
A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
8 Il dominera d’une mer à l’autre, Et du fleuve aux extrémités de la terre.
Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
9 Devant lui, les habitants du désert fléchiront le genou, Et ses ennemis lécheront la poussière.
Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
10 Les rois de Tarsis et des îles paieront des tributs, Les rois de Séba et de Saba offriront des présents.
Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
11 Tous les rois se prosterneront devant lui, Toutes les nations le serviront.
Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
12 Car il délivrera le pauvre qui crie, Et le malheureux qui n’a point d’aide.
Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
13 Il aura pitié du misérable et de l’indigent, Et il sauvera la vie des pauvres;
Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
14 Il les affranchira de l’oppression et de la violence, Et leur sang aura du prix à ses yeux.
Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
15 Ils vivront, et lui donneront de l’or de Séba; Ils prieront pour lui sans cesse, ils le béniront chaque jour.
Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
16 Les blés abonderont dans le pays, au sommet des montagnes, Et leurs épis s’agiteront comme les arbres du Liban; Les hommes fleuriront dans les villes comme l’herbe de la terre.
Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
17 Son nom subsistera toujours, Aussi longtemps que le soleil, son nom se perpétuera; Par lui on se bénira mutuellement, Et toutes les nations le diront heureux.
Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
18 Béni soit l’Éternel Dieu, le Dieu d’Israël, Qui seul fait des prodiges!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
19 Béni soit à jamais son nom glorieux! Que toute la terre soit remplie de sa gloire! Amen! Amen!
Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
20 Fin des prières de David, fils d’Isaï.
Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.