< Job 19 >

1 Job prit la parole et dit:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Jusques à quand affligerez-vous mon âme, Et m’écraserez-vous de vos discours?
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 Voilà dix fois que vous m’outragez; N’avez-vous pas honte de m’étourdir ainsi?
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 Si réellement j’ai péché, Seul j’en suis responsable.
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 Pensez-vous me traiter avec hauteur? Pensez-vous démontrer que je suis coupable?
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 Sachez alors que c’est Dieu qui me poursuit, Et qui m’enveloppe de son filet.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 Voici, je crie à la violence, et nul ne répond; J’implore justice, et point de justice!
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 Il m’a fermé toute issue, et je ne puis passer; Il a répandu des ténèbres sur mes sentiers.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 Il m’a dépouillé de ma gloire, Il a enlevé la couronne de ma tête.
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 Il m’a brisé de toutes parts, et je m’en vais; Il a arraché mon espérance comme un arbre.
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 Il s’est enflammé de colère contre moi, Il m’a traité comme l’un de ses ennemis.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 Ses troupes se sont de concert mises en marche, Elles se sont frayées leur chemin jusqu’à moi, Elles ont campé autour de ma tente.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 Il a éloigné de moi mes frères, Et mes amis se sont détournés de moi;
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 Je suis abandonné de mes proches, Je suis oublié de mes intimes.
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 Je suis un étranger pour mes serviteurs et mes servantes, Je ne suis plus à leurs yeux qu’un inconnu.
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 J’appelle mon serviteur, et il ne répond pas; Je le supplie de ma bouche, et c’est en vain.
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 Mon humeur est à charge à ma femme, Et ma plainte aux fils de mes entrailles.
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 Je suis méprisé même par des enfants; Si je me lève, je reçois leurs insultes.
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 Ceux que j’avais pour confidents m’ont en horreur, Ceux que j’aimais se sont tournés contre moi.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 Mes os sont attachés à ma peau et à ma chair; Il ne me reste que la peau des dents.
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 Ayez pitié, ayez pitié de moi, vous, mes amis! Car la main de Dieu m’a frappé.
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Pourquoi me poursuivre comme Dieu me poursuit? Pourquoi vous montrer insatiables de ma chair?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 Oh! Je voudrais que mes paroles fussent écrites, Qu’elles fussent écrites dans un livre;
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 Je voudrais qu’avec un burin de fer et avec du plomb Elles fussent pour toujours gravées dans le roc…
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 Mais je sais que mon rédempteur est vivant, Et qu’il se lèvera le dernier sur la terre.
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 Quand ma peau sera détruite, il se lèvera; Quand je n’aurai plus de chair, je verrai Dieu.
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 Je le verrai, et il me sera favorable; Mes yeux le verront, et non ceux d’un autre; Mon âme languit d’attente au-dedans de moi.
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 Vous direz alors: Pourquoi le poursuivions-nous? Car la justice de ma cause sera reconnue.
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 Craignez pour vous le glaive: Les châtiments par le glaive sont terribles! Et sachez qu’il y a un jugement.
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”

< Job 19 >