< Psaumes 58 >

1 Au chef des chantres. Al tachhêt. Mikhtam de David. Est-ce qu’en vérité, ô puissants, vous prononcez de justes arrêts, et jugez avec droiture les fils de l’homme!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
2 Non, de tout cœur vous pratiquez l’injustice; dans le pays, vous mettez en œuvre la violence de vos mains.
Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
3 Dès le sein de leur mère, les méchants sont fourvoyés; dès leur naissance, ils font fausse route, ceux qui débitent le mensonge.
Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
4 Ils ont du venin pareil au venin du serpent, de l’aspic sourd qui se bouche l’oreille,
Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
5 qui n’entend pas la voix des charmeurs, des magiciens les plus experts.
da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
6 O Dieu, brise-leur les dents dans la bouche; fracasse, ô Eternel, les crocs des lionceaux!
Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
7 Qu’ils se liquéfient comme de l’eau et s’écoulent! Que Dieu dirige ses flèches, pour qu’ils soient comme fauchés!
Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
8 Qu’ils soient comme un limaçon, qui se dissout en rampant; comme l’avorton d’une femme, qui n’a pas vu le soleil!
Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
9 Avant que vos marmites sentent la flamme des broussailles, que la tempête vienne tout enlever, qu’elles soient vertes encore ou déjà consumées!
Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
10 Le juste se réjouira, quand il verra les représailles; il baignera ses pas dans le sang des méchants.
Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
11 Et l’on dira: "Certes, il y a une récompense pour le juste; certes, il est une divinité exerçant la justice sur terre!"
Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”

< Psaumes 58 >