< Isaïe 49 >
1 Iles, écoutez-moi, et vous, peuples des contrées lointaines, soyez attentifs! L’Eternel m’a désigné dès le berceau; il a énoncé mon nom dès le sein de ma mère.
Ku kasa kunne gare ni, ku tsibirai; ku ji wannan, ku al’ummai masu nesa. Kafin a haife Ni Ubangiji ya kira ni; tun daga haihuwata ya ambaci sunana.
2 Il a rendu ma bouche semblable à un glaive tranchant et m’a abrité à l’ombre de sa main; il a fait de moi une flèche reluisante et m’a serré dans son carquois.
Ya yi bakina kamar takobi mai kaifi, cikin inuwar hannunsa ya ɓoye ni; ya sa na zama kamar kibiya mai tsini ya kuma ɓoye ni cikin kwarinsa.
3 Et il m’a dit: "Tu es mon serviteur; Israël, c’est par toi que je me couvre de gloire."
Ya ce mini, “Kai bawana ne, Isra’ila, a cikinka zan bayyana darajata.”
4 Cependant moi je pensais: "En vain je me suis fatigué, c’est pour le vide et le néant que j’ai dépensé ma force." Mais non, mon droit est auprès de l’Eternel, et ma récompense auprès de mon Dieu.
Amma na ce, “Na yi aiki a banza; na kashe duk ƙarfina a banza da wofi. Duk da haka abin da yake nawa yana a hannun Ubangiji, ladana kuma tana a wurin Allahna.”
5 Et maintenant, s’adressant à moi, l’Eternel qui m’a créé pour être son serviteur, pour lui ramener Jacob et grouper Israël autour de lui car grand est mon prix aux yeux de l’Eternel et mon Dieu est ma force,
Yanzu fa Ubangiji ya ce ya siffanta ni a cikin mahaifa don in zama bawansa don in dawo da Yaƙub gare shi in kuma tattara Isra’ila gare shi, gama an girmama ni a gaban Ubangiji Allahna kuma ne ƙarfina
6 l’Eternel me dit: "C’Est trop peu que tu sois mon serviteur, pour relever les tribus de Jacob et rétablir les ruines d’Israël; je veux faire de toi la lumière des nations, mon instrument de salut jusqu’aux confins de la terre."
ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
7 Ainsi parle l’Eternel, le libérateur d’Israël, son Saint, à celui qui est un objet de mépris pour les hommes, de répulsion pour les peuples, à l’esclave des puissants: "Des rois, en le voyant, se lèveront, des princes se prosterneront, par égard pour l’Eternel, qui est fidèle à ses promesses, du Saint d’Israël qui t’a élu."
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansa da kuma Mai Tsarkin nan na Isra’ila gare shi wanda al’ummai suka rena suka kuma ki, ga bawan masu mulki. “Sarakuna za su gan ka su kuma miƙe tsaye, sarakuna za su gani su kuma rusuna, saboda Ubangiji, wanda yake mai aminci, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, wanda ya zaɓe ka.”
8 Ainsi parle l’Eternel: "À l’heure de la clémence, je t’exauce; au jour du salut, je viens à ton secours. Je veille sur toi, je fais de toi un gage d’alliance parmi les nations, pour restaurer la terre et restituer les patrimoines en ruines,
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “A lokacin tagomashina zan amsa muku, kuma a ranar ceto zan taimake ku; zan kiyaye ku zan kuma sa ku zama alkawari ga mutane, don ku maido da ƙasa ku kuma sāke raba gādon kufai,
9 pour dire aux prisonniers: Sortez! à ceux qui sont retenus dans les ténèbres: Paraissez au grand jour! Ils se nourriront sur les routes et trouveront une pâture sur toutes les hauteurs dénudées.
don ku ce wa waɗanda suke cikin kurkuku, ‘Ku fito,’ ga waɗanda suke cikin duhu kuma, ‘Ku’yantu!’ “Za su yi kiwo kusa da hanyoyi su kuma sami wurin kiwo a kowane tudu.
10 Ils n’éprouveront ni faim ni soif; ni sécheresse ni soleil brûlant ne les feront souffrir, car Celui qui les a pris en pitié les dirigera et les mènera près des sources d’eau.
Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba, ba kuwa zafin hamada ko rana ta buge su ba. Shi da ya yi musu jinƙai zai jagorance su ya kuma bishe su kusa da maɓulɓulan ruwa.
11 Je transformerai toutes mes montagnes en chemins faciles, et mes routes seront rehaussées.
Zan mayar da dukan duwatsu su zama hanyoyi, a kuma gyara manyan hanyoyina.
12 Voici venir les uns de pays éloignés, voici venir les autres du Septentrion et du Couchant, d’autres arrivent du pays de Sinnîm.
Duba, za su zo daga nesa waɗansu daga arewa, waɗansu daga yamma, waɗansu daga yankin Aswan.”
13 Cieux, jubilez, terre, sois dans l’allégresse, et vous, montagnes, entonnez des chants joyeux! Car Dieu console son peuple, il prend en pitié ses humbles."
Ku yi sowa don farin ciki, ya ku sammai; ki yi farin ciki, ya ke duniya; ku ɓarke da waƙa, ya ku duwatsu! Gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa zai kuma ji tausayin mutanensa da suke shan wahala.
14 Sion avait dit: "L’Eternel m’a délaissée, le Seigneur m’a oubliée."
Amma Sihiyona ta ce, “Ubangiji ya yashe ni, Ubangiji ya manta da ni.”
15 Est-ce qu’une femme peut oublier son nourrisson, ne plus aimer le fruit de ses entrailles? Fût-elle capable d’oublier, moi je ne t’oublie point!
“Yana yiwuwa mahaifiya ta manta da jariri a ƙirjinta ta kuma kāsa nuna tausayi ga yaron da ta haifa? Mai yiwuwa ta manta, amma ba zan taɓa manta da ke ba!
16 Oui, j’ai gravé ton nom sur la paume de mes mains, tes remparts sont constamment devant mes yeux.
Duba, na zāna ki a tafin hannuwana; katangarki kullum suna a gabana.
17 Tes enfants s’empressent d’accourir; tes destructeurs et les auteurs de ta ruine s’éloignent de toi.
’Ya’yanki maza su komo da gaggawa, waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su bar ki.
18 Porte tes regards à l’entour et vois: tous en masse ils te reviennent! Vrai comme je suis vivant, dit l’Eternel, tu les revêtiras tous comme une parure, tu te ceindras d’eux comme une fiancée.
Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye; dukan’ya’yanki sun taru suka kuma dawo gare ki. Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “Za ki yafa su duka kamar kayan ado; za ki yi ado da su, kamar amarya.
19 Oui, tes ruines, tes solitudes, cette terre couverte de tes décombres, elles seront trop étroites pour leurs habitants; mais tes exploiteurs auront fui loin de toi.
“Ko da yake an lalatar da ke aka kuma mai da ke kufai ƙasarki kuma ta zama kango, yanzu za ki kāsa sosai saboda yawan mutanenki, kuma waɗanda suka cinye ki za su kasance can da nisa.
20 Un jour, ces enfants que tu croyais perdus, tu les entendras dire: "Je suis à l’étroit en ces lieux, fais-moi place pour que je m’établisse."
’Ya’yan da aka haifa a lokacin baƙin cikinki za su ce a kunnenki, ‘Wannan wuri ya yi mana kaɗan ƙwarai; ki ƙara mana wurin zama.’
21 Et tu diras en ton cœur: "Qui me les a enfantés, tous ceux-là, à moi qui étais privée d’enfants et solitaire? J’Étais proscrite et délaissée, ceux-là, qui les a élevés? J’Étais demeurée seule, ceux-là, où étaient-ils?"
Sa’an nan za ki ce a zuciyarki, ‘Wa ya haifa waɗannan? Na yi baƙin ciki na kuma zama wadda ba ta haihuwa; an yi mini daurin talala aka kuma ƙi ni. Wane ne ya yi renon waɗannan? An bar ni ni kaɗai, amma waɗannan, ina suka fito?’”
22 Ainsi parle le Seigneur-Eternel: "Voici, j’étendrai ma main sur les nations, et du côté des peuples je dresserai ma bannière; et ils apporteront tes fils dans leur giron, et ils chargeront tes filles sur leurs épaules.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe’ya’yanki mata a kafaɗunsu.
23 Des rois seront tes nourriciers, et leurs princesses tes nourrices; leur front jusqu’à terre se courbera devant toi, et ils baiseront la poussière de tes pieds. Et tu reconnaîtras que je suis l’Eternel, qui ne trompe jamais l’attente de ceux qui espèrent en moi."
Sarakuna za su zama kamar iyayen reno, sarauniyoyinsu kuma za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna a gabanki da fuskokinsu har ƙasa; za su lashe ƙura a ƙafafunki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji; waɗanda suke sa zuciya gare ni ba za su sha kunya ba.”
24 Quoi! Arrachera-t-on au fort son butin? La capture faite aux dépens du juste sera-t-elle reprise?
Za a iya ƙwace ganima daga jarumawa, ko a kuɓutar da kamammu daga hannun marasa tsoro?
25 Or, ainsi parle l’Eternel: "Oui, le butin du fort lui sera arraché; oui, la capture du tyran lui échappera! Car moi-même je serai ton champion contre tes adversaires, et je porterai secours à tes enfants.
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci’ya’yanki.
26 Et je ferai dévorer à tes persécuteurs leur propre chair, et ils s’enivreront de leur sang comme d’un vin exquis; et toute créature saura que c’est moi, l’Eternel, qui te protège, que ton libérateur est le Puissant de Jacob."
Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”