< Ézéchiel 15 >

1 La parole du Seigneur me fut adressée en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 "Fils de l’homme, qu’adviendra-t-il du bois de la vigne parmi tous les bois, du sarment qui se trouve dans les arbres de la forêt?
“Ɗan mutum, da me itacen kuringa ya fi reshen waɗansu itatuwa kyau a cikin kurmi?
3 Est-ce qu’on en prendra du bois pour le travailler, en fera-t-on des chevilles, pour y suspendre quelque ustensile?
An taɓa ɗaukan itacensa an yi wani abu mai amfani? Akan yi maratayi da ita da za a rataya wani abu a kai?
4 Voici qu’on l’a donné en aliment au feu; les deux bouts, le feu les a consumés et le dedans en est noirci: pourra-t-il être de quelque usage?
Bayan kuma a jefa ta cikin wuta, wuta kuma ta cinye kowane gefe ta kuma babbaka tsakiyarta, tana da amfani don yin wani abu kuma?
5 Quoi! Quand il était intact, on ne l’employait à rien; maintenant que le feu l’a consumé et noirci, il serait encore de quelque usage?
In ba ta da amfanin wani abu sa’ad da take cikakkiya, balle bayan da wuta ta babbake ta, za a iya yin amfani da ita?
6 C’Est pourquoi, ainsi a dit le Seigneur Dieu, tel le bois de la vigne parmi les bois de la forêt, que j’ai donné en aliment au feu, ainsi je traite les habitants de Jérusalem.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kamar yadda na ba da itacen kuringa a cikin itatuwan kurmi ya zama itacen wuta, haka zan sa mazaunan Urushalima su zama.
7 Je dirigerai ma face contre eux: ils sont sortis du feu et le feu les consumera, et vous saurez que je suis l’Eternel quand je tournerai ma face contre eux.
Zan yi gāba da su. Ko da yake sun fito daga wuta, wuta za tă cinye su. Kuma sa’ad da na yi gāba da su, za ku san cewa ni ne Ubangiji.
8 Et je ferai de leur terre une désolation, parce qu’ils se sont montrés infidèles," dit le Seigneur Dieu.
Zan mai da ƙasar kufai domin sun yi rashin aminci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ézéchiel 15 >