< Psaumes 92 >

1 Psaume. Cantique pour le jour du sabbat. Il est bon de louer Yahweh, et de célébrer ton nom, ô Très-Haut,
Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
2 de publier le matin ta bonté, et ta fidélité pendant la nuit,
don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
3 sur l’instrument à dix cordes et sur le luth, avec les accords de la harpe.
da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
4 Tu me réjouis, Yahweh, par tes œuvres, et je tressaille devant les ouvrages de tes mains.
Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
5 Que tes œuvres sont grandes, Yahweh, que tes pensées sont profondes!
Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
6 L’homme stupide n’y connaît rien, et l’insensé n’y peut rien comprendre.
Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
7 Quand les méchants croissent comme l’herbe, et que fleurissent tous ceux qui font le mal, c’est pour être exterminés à jamais.
cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
8 Mais toi, tu es élevé pour l’éternité, Yahweh!
Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
9 Car voici que tes ennemis, Yahweh, voici que tes ennemis périssent, tous ceux qui font le mal sont dispersés.
Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
10 Et tu élèves ma corne, comme celle du buffle, je suis arrosé avec une huile fraîche.
Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
11 Mon œil se plaît à contempler mes ennemis, et mon oreille à entendre les méchants qui s’élèvent contre moi.
Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
12 Le juste croîtra comme le palmier, il s’élèvera comme le cèdre du Liban.
Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
13 Plantés dans la maison de Yahweh, ils fleuriront dans les parvis de notre Dieu.
da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
14 Ils porteront encore des fruits dans la vieillesse; ils seront pleins de sève et verdoyants,
Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
15 pour proclamer que Yahweh est juste: il est mon rocher, et il n’y a pas en lui d’injustice.
suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”

< Psaumes 92 >