< Psaumes 5 >
1 Au maître de chant. Sur les flûtes. Psaume de David. Prête l’oreille à mes paroles, Yahweh, entends mes soupirs;
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Busa. Ta Dawuda. Ka saurare kalmomina, ya Ubangiji, ka ji ajiyar zuciyata.
2 sois attentif à mes cris, ô mon Roi et mon Dieu; car c’est à toi que j’adresse ma prière.
Ka saurare kukata na neman taimako, Sarkina da Allahna, gama gare ka nake addu’a.
3 Yahweh, dès le matin, tu entends ma voix; dès le matin, je t’offre mes vœux et j’attends.
Da safe, ya Ubangiji, ka ji muryata; da safe na gabatar da bukatuna a gabanka in kuma jira da sa zuciya.
4 Car tu n’es pas un Dieu qui prenne plaisir au mal; avec toi le méchant ne saurait habiter.
Kai ba Allahn da yake jin daɗin mugu ba ne; gama kana gāba da dukan masu aikata mugunta.
5 Les insensés ne subsistent pas devant tes yeux; tu hais tous les artisans d’iniquité.
Masu fariya ba za su iya tsaya a gabanka ba. Kana ƙin duk masu aikata abin da ba daidai ba.
6 Tu fais périr les menteurs; Yahweh abhorre l’homme de sang et de fraude.
Kakan hallaka masu yin ƙarya. Masu kisankai da mutane masu ruɗu Ubangiji yana ƙyama.
7 Pour moi, par ta grande miséricorde, j’irai dans ta maison; je me prosternerai, dans ta crainte, devant ton saint temple.
Amma ni, ta wurin jinƙanka mai girma, zan shiga gidanka; da bangirma zan durƙusa ga haikalinka.
8 Seigneur, conduis-moi, dans ta justice, à cause de mes ennemis aplanis ta voie sous mes pas.
Ka bi da ni, ya Ubangiji, cikin adalcinka saboda abokan gābana, ka fayyace hanyarka a gabana.
9 Car il n’y a pas de sincérité dans leur bouche; leur cœur n’est que malice; leur gosier est un sépulcre ouvert, leur langue se fait caressante.
Babu ko kalma guda daga bakinsu da za a dogara da ita; marmarinsu kawai shi ne su hallakar da waɗansu. Maƙogwaronsu buɗaɗɗen kabari ne; da harshensu suna faɗin ƙarya.
10 Châtie-les, ô Dieu. Qu’ils échouent dans leurs desseins! A cause de leurs crimes sans nombre, précipite-les; car ils sont en révolte contre toi.
Ka furta su masu laifi, ya Allah! Bari makircinsu yă zama fāɗuwarsu. Ka kore su saboda yawan zunubansu, saboda sun tayar maka.
11 Alors se réjouiront tous ceux qui se confient en toi; ils seront dans une perpétuelle allégresse, et tu les protégeras; ils se livreront à de joyeux transports, ceux qui aiment ton nom.
Amma bari dukan waɗanda suke neman mafaka gare ka su yi murna; bari kullum su yi ta rerawa saboda farin ciki. Ka buɗe kāriyarka a bisansu, domin waɗanda suke ƙaunar sunanka su yi farin ciki a cikinka.
12 Car tu bénis le juste, Yahweh; tu l’entoures de bienveillance comme d’un bouclier.
Gama tabbatacce, ya Ubangiji, kakan albarkaci adalai; kakan kewaye su da tagomashinka kamar garkuwa.