< Job 32 >
1 Ces trois hommes cessèrent de répondre à Job, parce qu’il persistait à se regarder comme juste.
Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
2 Alors s’alluma la colère d’Eliu, fils de Barachel le Bouzite, de la famille de Ram. Sa colère s’alluma contre Job, parce qu’il se prétendait plus juste que Dieu.
Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
3 Elle s’alluma aussi contre ses trois amis, parce qu’ils n’avaient pas trouvé de bonnes réponse à lui faire et que néanmoins ils condamnaient Job.
Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
4 Comme ils étaient plus âgés que lui, Eliu avait attendu pour parler à Job.
Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
5 Mais voyant qu’il n’y avait plus de réponse dans la bouche de ces trois hommes, il s’enflamma de colère.
Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
6 Alors Eliu, fils de Barachel le Bouzite, prit la parole et dit: Je suis jeune et vous êtes des vieillards; c’est pourquoi j’étais effrayé et je redoutais de vous faire connaître mon sentiment.
Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
7 Je me disais: « Les jours parleront, les nombreuses années révéleront la sagesse. »
Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
8 Mais c’est l’esprit mis dans l’homme, le souffle du Tout-Puissant qui lui donne l’intelligence.
Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
9 Ce n’est pas l’âge qui donne la sagesse, ce n’est pas la vieillesse qui discerne la justice.
Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
10 Voilà pourquoi je dis: « Écoutez-moi; je vais, moi aussi, exposer ma pensée. »
“Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
11 J’ai attendu tant que vous parliez, j’ai prêté l’oreille à vos raisonnements, jusqu’à la fin de vos débats.
Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
12 Je vous ai suivis attentivement, et nul n’a convaincu Job, nul d’entre vous n’a réfuté ses paroles.
na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
13 Ne dites pas: « Nous avons trouvé la sagesse; c’est Dieu qui le frappe, et non pas l’homme. »
Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
14 Il n’a pas dirigé contre moi ses discours, mais ce n’est pas avec vos paroles que je lui répondrai.
Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
15 Les voilà interdits; ils ne répondent rien; la parole leur fait défaut.
“Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
16 J’ai attendu qu’ils eussent fini de parler, qu’ils restassent muets et sans réponse.
Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
17 C’est à mon tour de parler à présent; je veux dire aussi ce que je pense.
Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
18 Car je suis plein de discours, l’esprit qui est en moi m’oppresse.
Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
19 Mon cœur est comme un vin renfermé, comme une outre remplie de vin nouveau qui va éclater.
a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
20 Que je parle donc, afin de respirer à l’aise, que mes lèvres s’ouvrent pour répondre!
Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
21 Je ne veux faire acception de personne, je ne flatterai qui que ce soit.
Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
22 Car je ne sais pas flatter; autrement mon Créateur m’enlèverait sur-le-champ.
gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.