< Job 20 >
1 Alors Sophar de Naama prit la parole et dit:
Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 C’est pourquoi mes pensées me suggèrent une réponse, et, à cause de mon agitation, j’ai hâte de la donner.
“Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
3 J’ai entendu des reproches qui m’outragent; dans mon intelligence, mon esprit trouvera la réplique.
Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
4 Sais-tu bien que, de tout temps, depuis que l’homme a été placé sur la terre,
“Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
5 le triomphe des méchants a été court, et la joie de l’impie d’un moment?
mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
6 Quand il porterait son orgueil jusqu’au ciel, et que sa tête toucherait aux nues,
Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
7 comme son ordure, il périt pour toujours; ceux qui le voyaient disent: « Où est-il? »
Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
8 Il s’envole comme un songe, et on ne le trouve plus; il s’efface comme une vision de la nuit.
Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
9 L’œil qui le voyait ne le découvre plus; sa demeure ne l’apercevra plus.
Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
10 Ses enfants imploreront les pauvres, de ses propres mains il restituera ses rapines.
Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
11 Ses os étaient pleins de ses iniquités cachées; elles dormiront avec lui dans la poussière.
Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
12 Parce que le mal a été doux à sa bouche, qu’il l’a caché sous sa langue,
“Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
13 qu’il l’a savouré sans l’abandonner, et l’a retenu au milieu de son palais:
ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
14 sa nourriture tournera en poison dans ses entrailles, elle deviendra dans son sein le venin de l’aspic.
duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
15 Il a englouti des richesses, il les vomira; Dieu les retirera de son ventre.
Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
16 Il a sucé le venin de l’aspic, la langue de la vipère le tuera.
Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
17 Il ne verra jamais couler les fleuves, les torrents de miel et de lait.
Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
18 Il rendra ce qu’il a gagné et ne s’en gorgera pas, dans la mesure de ses profits, et il n’en jouira pas.
Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
19 Car il a opprimé et délaissé les pauvres, il a saccagé leur maison, et ne l’a pas rétablie:
Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
20 son avidité n’a pu être rassasiée, il n’emportera pas ce qu’il a de plus cher.
“Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
21 Rien n’échappait à sa voracité; aussi son bonheur ne subsistera pas.
Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
22 Au sein de l’abondance, il tombe dans la disette; tous les coups du malheur viennent sur lui.
Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
23 Voici pour lui remplir le ventre: Dieu enverra sur lui le feu de sa colère, elle pleuvra sur lui jusqu’en ses entrailles.
Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
24 S’il échappe aux armes de fer, l’arc d’airain le transperce.
Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
25 Il arrache le trait, il sort de son corps, l’acier sort étincelant de son foie; les terreurs de la mort tombent sur lui.
Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
26 Une nuit profonde engloutit ses trésors; un feu que l’homme n’a pas allumé le dévore, et consume tout ce qui restait dans sa tente.
duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
27 Les cieux révéleront son iniquité, et la terre s’élèvera contre lui.
Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
28 L’abondance de sa maison sera dispersée, elle disparaîtra au jour de la colère.
Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
29 Telle est la part que Dieu réserve au méchant, et l’héritage que lui destine Dieu.
Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”