< Isaïe 48 >

1 Ecoutez ceci, maison de Jacob, vous qui êtes appelés du nom d’Israël, et qui êtes sortis de la source de Juda; vous qui jurez par le nom de Yahweh, et qui célébrez le Dieu d’Israël, mais sans sincérité ni droiture.
“Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
2 Car ils tirent leur nom de la ville sainte, et ils s’appuient sur le Dieu d’Israël, dont le nom est Yahweh des armées.
ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
3 Dès longtemps, j’ai annoncé les premières choses; elles sortirent de ma bouche; je les proclamai; soudain j’ai agi, et elles sont arrivées.
na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
4 Comme je savais que tu es dur, que ton cou est une barre de fer, et que ton front est d’airain,
Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
5 je t’ai annoncé ces choses il y a longtemps; je te les ai déclarées avant qu’elles n’arrivent, de peur que tu ne dises: « Mon idole les a faites; mon dieu de bois ou de fonte les a ordonnées. »
Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
6 Tu l’as entendu; vois, tout s’est accompli; mais vous, ne le déclarerez-vous pas? Maintenant, je te fais entendre des choses nouvelles, cachées, que tu ne connais point.
Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
7 C’est maintenant qu’elles sont créées, et non auparavant; jusqu’à ce jour, tu n’en avais pas entendu parler, de peur que tu ne dises: « Voici, je le savais! »
Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
8 Tu n’en as rien entendu, tu n’en as rien su; jamais ton oreille n’en a rien perçu, parce que je savais que tu es tout à fait infidèle, que ton nom est Prévaricateur dès le sein de ta mère.
Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
9 A cause de mon nom, je retiens ma colère, et à cause de ma gloire, je patiente avec toi, pour ne pas t’exterminer.
Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
10 Voici, je t’ai fondu, mais sans obtenir l’argent; je t’ai éprouvé au creuset de l’affliction.
Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
11 C’est pour l’amour de moi, pour l’amour de moi que je le fais; car comment mon nom serait-il profané? Je ne donnerai pas ma gloire à un autre.
Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
12 Ecoute-moi, Jacob, et toi, Israël, que j’ai appelé; c’est moi, moi qui suis le premier, moi aussi qui suis le dernier.
“Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
13 C’est aussi ma main qui a fondé la terre, et ma droite qui a étendu les cieux; c’est moi qui les appelle, et aussitôt ils se présentent.
Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
14 Assemblez-vous tous et écoutez: qui d’entre eux a annoncé ces choses? — Celui qu’aime Yahweh accomplira sa volonté dans Babel, et son bras sera contre les Chaldéens. —
“Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
15 Moi, moi, j’ai parlé, et je l’ai appelé; je l’ai fait venir, et sa voie sera prospère.
Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
16 Approchez-vous de moi, entendez ceci: Dès l’origine je n’ai pas parlé en cachette; depuis que ces choses arrivent, je suis là; — Et maintenant le Seigneur Yahweh m’envoie avec son Esprit. —
“Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
17 Ainsi parle Yahweh, ton rédempteur, le Saint d’Israël: Moi, Yahweh, ton Dieu, je t’enseigne pour ton bien, je te conduis dans le chemin où tu dois marcher.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
18 Oh! sois attentif à mes commandements, et ta paix sera comme un fleuve, ta justice comme les flots de la mer;
Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
19 ta postérité sera comme le sable et le fruit de tes entrailles comme les grains de sable; son nom ne sera ni retranché ni effacé devant moi.
Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
20 Sortez de Babylone, fuyez les Chaldéens avec des cris de joie! Publiez-le, proclamez-le, faites-le savoir jusqu’à l’extrémité de la terre! Dites: « Yahweh a racheté son serviteur Jacob!
Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
21 Ils n’ont pas soif dans le désert où il les a conduits; il fait couler pour eux l’eau du rocher; il fend le rocher, et les eaux jaillissent! »
Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
22 Il n’y a pas de paix pour les méchants, dit Yahweh.
“Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.

< Isaïe 48 >