< Isaïe 28 >

1 Malheur à l’orgueilleux diadème des buveurs d’Ephraïm, à la fleur éphémère qui fait l’éclat de leur parure, sur les sommets de la fertile vallée des hommes ivres de vin.
Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
2 Voici qu’un ennemi fort et puissant vient de la part du Seigneur, comme une averse de grêle, un ouragan destructeur; comme une averse de grosses eaux qui débordent, il le jettera par terre avec violence.
Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
3 Il sera foulé aux pieds l’orgueilleux diadème des buveurs d’Ephraïm,
Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
4 et il en sera de la fleur éphémère qui fait l’éclat de leur parure, au sommet de la fertile vallée, comme d’une figue mûrie avant l’été; celui qui l’aperçoit, l’a à peine dans la main, qu’il l’avale.
Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
5 En ce jour-là, Yahweh sera un brillant diadème, et une couronne de gloire pour le reste de son peuple;
A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
6 un esprit de justice pour celui qui siège pour la justice, une force pour ceux qui repoussent l’assaut à la porte.
Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
7 Eux aussi sont troublés par le vin, égarés par les boissons fortes, prêtre et prophète sont égarés par les boissons fortes; ils sont noyés dans le vin, égarés par les boissons fortes; ils sont troublés en prophétisant, ils vacillent en jugeant,
Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
8 toutes les tables sont couvertes d’immondes vomissements, il n’y a plus de place.
Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
9 « A qui veut-il enseigner la sagesse, et à qui veut-il faire comprendre la leçon? A des enfants à peine sevrés, à peine détachés de la mamelle?
“Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
10 Car c’est ordre sur ordre, ordre sur ordre, règle sur règle, règle sur règle, tantôt ceci, tantôt cela. »
Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
11 Eh bien, c’est par des gens qui balbutient, et dans une langue étrangère, que Yahweh parlera à ce peuple.
To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
12 Il avait dit: « Voici le lieu du repos: laissez reposer celui qui est fatigué; voici le soulagement; » mais ils n’ont pas voulu entendre.
waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
13 La parole de Yahweh sera donc pour eux ordre sur ordre, ordre sur ordre, règle sur règle, règle sur règle; tantôt ceci, tantôt cela, afin qu’ils aillent, et tombent à la renverse, qu’ils se brisent, qu’ils soient pris au filet.
Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
14 C’est pourquoi écoutez la parole de Yahweh, hommes moqueurs, chefs de ce peuple qui est à Jérusalem.
Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
15 Vous dites: « Nous avons fait un pacte avec la mort, nous avons fait une convention avec le schéol. Le fléau débordant passera et ne nous atteindra pas; car nous nous sommes fait du mensonge un refuge, et de la fraude un abri. » (Sheol h7585)
Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol h7585)
16 C’est pourquoi ainsi parle le Seigneur Yahweh: Voici que j’ai mis pour fondement en Sion une pierre, une pierre éprouvée, angulaire, de prix, solidement posée: qui s’appuiera sur elle avec foi ne fuira pas.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
17 Je prendrai le droit pour règle, et la justice pour niveau. Et la grêle balaiera le refuge de mensonge, et les eaux emporteront votre abri.
Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
18 Votre pacte avec la mort sera anéanti, et votre convention avec le schéol ne subsistera pas; quand le fléau débordant passera, il vous écrasera; (Sheol h7585)
Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol h7585)
19 aussi souvent qu’il passera, il vous saisira. Car il passera demain et demain, le jour et la nuit; la terreur seule vous fera la leçon!
A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
20 Car « le lit est trop court pour s’y étendre, et la couverture trop étroite pour s’en envelopper. »
wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
21 Car Yahweh se lèvera comme à la montagne de Pharasim; il frémira d’indignation comme dans la vallée de Gabaon, pour accomplir son œuvre, œuvre singulière, pour exécuter son travail, travail étrange!
Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
22 Et maintenant, cessez de vous moquer, de peur que vos liens ne se resserrent; car une destruction est résolue, — je l’ai entendu, — par Yahweh des armées, contre toute la terre.
Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
23 Prêtez l’oreille et entendez ma voix, soyez attentifs et entendez ma parole.
Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
24 Le laboureur, pour semer, est-il toujours à labourer, à ouvrir et à herser sa terre?
Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
25 Ne va-t-il pas, quand il en a aplani la surface, jetter la nigelle, semer le cumin, mettre le froment en lignes, l’orge à sa place, et l’épeautre en bordure?
Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
26 C’est son Dieu qui lui enseigne ces règles, et qui l’instruit.
Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
27 Car ce n’est pas avec le traîneau qu’on foule la nigelle et la roue du chariot ne passe pas sur le cumin; mais on bat la nigelle avec le bâton, et le cumin avec la verge.
Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
28 On foule le froment, mais on se garde de le battre toujours; on y pousse la roue du chariot, et les chevaux, mais sans le broyer.
Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
29 Cela aussi vient de Yahweh des armées; il est admirable en ses conseils et riche en ses moyens.
Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.

< Isaïe 28 >