< Psalmien 137 >

1 Babelin virtain tykönä me istuimme ja itkimme, kuin me Zionin muistimme.
A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
2 Kanteleemme me ripustimme pajuihin, jotka siellä olivat.
A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
3 Siellä he käskivät meidän veisata, jotka meitä vankina pitivät, ja iloita meidän itkussamme: Veisatkaat meille Zionin virsiä.
gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
4 Kuinka me veisaisimme Herran veisun vieraalla maalla?
Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
5 Jos minä unohdan sinua, Jerusalem, niin olkoon oikia käteni unohdettu.
In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
6 Tarttukoon kieleni suuni lakeen, ellen minä sinua muista, ellen minä tee Jerusalemia ylimmäiseksi ilokseni.
Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
7 Herra, muista Edomin lapsia Jerusalemin päivänä, jotka sanovat: repikäät maahan hamaan hänen perustukseensa asti.
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
8 Sinä hävitetty tytär, Babel; autuas on, se joka sinulle kostaa, niinkuin sinä meille tehnyt olet.
Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
9 Autuas on se, joka piskuiset lapses ottaa ja paiskaa kiviin.
shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.

< Psalmien 137 >