< 1 Aikakirja 13 >
1 Ja David piti neuvoa tuhanten ja satain pääruhtinain ja kaikkein päämiesten kanssa.
Sai Dawuda ya tattauna da kowane ɗaya daga cikin shugabanninsa, shugabannin sojoji na dubu-dubu da na ɗari-ɗari.
2 Ja David sanoi kaikelle Israelin joukoille: jos teille kelpaa, ja jos se on Herralta meidän Jumalaltamme, niin toimittakaamme kaikella muotoa menemään muiden meidän veljeimme tykö koko Israelin maahan, ja pappein ja Leviläisten tykö kaupunkeihin, joissa esikaupungit ovat, että he kokoontuisivat meidän tykömme,
Sa’an nan ya ce wa dukan taron Isra’ila, “In ya yi muku kyau kuma in nufin Ubangiji Allahnmu ne, bari mu aika da saƙo nesa da kuma ko’ina zuwa ga sauran’yan’uwanmu a duk iyakokin Isra’ila, da kuma zuwa ga firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a garuruwansu da makiyayansu, su zo wurinmu.
3 Ja noutakaamme Jumalamme arkki meidän tykömme; sillä emme Saulin aikana siitä lukua pitäneet.
Bari mu ɗauko akwatin alkawarin Allahnmu mu kawo wurinmu, gama ba mu neme shi a lokacin mulkin Shawulu ba.”
4 Niin kaikki joukko vastasi, että niin piti tehtämän; sillä se kelpasi kaikelle kansalle.
Dukan taron jama’a suka yarda su yi haka, domin ya yi daidai ga dukan mutane.
5 Niin David kokosi kaiken Israelin, Egyptin Siihorista aina Hamatiin asti, noutamaan Jumalan arkkia Kirjatjearimista.
Saboda haka Dawuda ya tattara dukan Isra’ilawa, daga Kogin Shihor a Masar zuwa Lebo Hamat, don su kawo akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim.
6 Ja David meni ja kaikki Israel Baalatiin, Kirjatjearimiin, joka on Juudassa, noutamaan sieltä Herran Jumalan arkkia, joka Kerubimin päällä istuu, jonka nimeä rukoillaan.
Dawuda da dukan Isra’ilawa tare da shi suka tafi Ba’ala na Yahuda (Kiriyat Yeyarim) don su haura daga can su kawo akwatin alkawarin Allah Ubangiji, wanda yake zama tsakanin kerubobi, akwatin alkawarin da ake kira da Sunan.
7 Ja he panivat Jumalan arkin uuteen vaunuun, veivät sen Abinadabin huoneesta, ja Ussa ja Ahio ajoivat vaunua.
Suka ɗauki akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab a kan sabon keken shanu, Uzza da Ahiyo ne suke lura da shi.
8 Mutta David ja kaikki Israel iloitsivat Jumalan edessä kaikesta voimastansa, lauluilla, kanteleilla, psaltareilla, trumpuilla, symbaleilla ja basunilla.
Dawuda da dukan Isra’ilawa suka yi shagali da dukan ƙarfinsu a gaban Allah, tare da waƙoƙi da garayu, molaye, ganguna, kuge da ƙahoni.
9 Ja he tulivat Kidonin lakeudelle, niin ojensi Ussa kätensä arkkia pitelemään; sillä härjät poikkesivat sivulle.
Sa’ad da suka kai masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa don yă gyara akwatin alkawarin, gama shanun sun yi tuntuɓe.
10 Niin Herran viha julmistui Ussan päälle ja löi häntä, että hän ojensi kätensä arkkia pitämään, niin että hän siinä kuoli Jumalan edessä.
Sai fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Uzza, ya kuma buge shi domin ya sa hannunsa a kan akwatin alkawarin. Sai ya mutu a can a gaban Allah.
11 Niin David tuli murheelliseksi, että Herra Ussan repäisi rikki. Ja hän kutsui sen paikan Perets-ussa tähän päivään asti,
Ran Dawuda ya ɓace domin Ubangiji ya husata a kan Uzza, kuma har wa yau ana ce da wannan wuri Ferez Uzza.
12 Ja David pelkäsi Jumalaa sinä päivänä ja sanoi: kuinka minun pitää viemän Jumalan arkin minun tyköni?
Dawuda ya ji tsoron Allah a wannan rana ya kuma yi tambaya, “Yaya zan taɓa kawo akwatin alkawarin Allah gare ni?”
13 Sentähden ei David antanut viedä Jumalan arkkia tykönsä Davidin kaupunkiin, vaan antoi poiketa Obededomin Gatilaisen huoneesen.
Don haka bai ɗauki akwatin alkawarin ya kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka, ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
14 Ja Jumalan arkki viipyi Obededomin tykönä hänen huoneessansa kolme kuukautta. Ja Herra siunasi Obededomin huoneen ja kaikki mitä hänellä oli.
Akwatin Alkawarin Allah ya zauna tare da iyalin Obed-Edom a gidansa wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkaci gidan Obed-Edom da kome da yake da shi.