< Luke 23 >

1 Then they all rose in a body and led Jesus before Pilate.
Sai duk taron suka tashi, suka kawo Yesu gaban Bilatus.
2 And they began to accuse him: “This is a man whom we found misleading our people, preventing them from paying taxes to the Emperor, and giving out that he himself is ‘Christ, a King.’”
Suka fara saransa, cewa “Mun same wannan mutum yana ruda kasarmu, ya haramta a ba Kaisar haraji, yana kuma cewa shi da kansa ne Almasihu, sarki.”
3 “Are you the King of the Jews?” Pilate asked him. “It is true,” replied Jesus.
Bilatus ya tambaye shi, cewa “Shin kaine Sarkin Yahudawa?” Sai Yesu ya amsa masa ya ce, “Haka ka ce.”
4 But Pilate, turning to the Chief Priests and the people, said: “I do not see anything to find fault with in this man.”
Sai Bilatus ya ce wa manyan firistocin da taro mai yawa, “Ban samu ko laifi daya game da wannan mutumin ba.”
5 But they insisted: “He is stirring up the people by his teaching all through Judea; he began with Galilee and has now come here.”
Amma suka yi ta cewa, “Yana ta da hankalin mutane da koyarwa a dukan Yahudiya, ya fara daga Galili har zuwa ga wannan wuri.”
6 Hearing this, Pilate asked if the man was a Galilean;
Sa'adda Bilatus ya ji wannan, sai ya tambaya ko mutumin daga Galiline.
7 and, having satisfied himself that Jesus came under Herod’s jurisdiction, he sent him to Herod, who also was at Jerusalem at the time.
Sa'adda ya gane cewa yana karkashin mulkin Hirudus, sai ya tura Yesu wurin Hirudus, wanda shi da kansa yana Urushalima a wadannan kwanakin.
8 When Herod saw Jesus, he was exceedingly pleased, for he had been wanting to see him for a long time, having heard a great deal about him; and he was hoping to see some sign given by him.
Sa'adda Hirudus ya ga Yesu, sai ya cika da farin ciki sosai, saboda ya so ganinsa tunda dadewa. Tun can ya ji game da shi sai ya yi begen ganin wadansu al'ajibai da zai yi.
9 So he questioned him at some length, but Jesus made no reply.
Hirudus ya tambaye Yesu cikin kalmomi masu yawa, amma Yesu bai amsa masa da komai ba.
10 Meanwhile the Chief Priests and the Teachers of the Law stood by and vehemently accused him.
Sai manyan firistoci da marubuta suka tsaya, suna ta yi masa zargi mai zafi.
11 And Herod, with his soldiers, treated Jesus with scorn; he mocked him by throwing a gorgeous robe round him, and then sent him back to Pilate.
Hirudus da sojojinsa suka zarge shi, suka kuma yi masa ba'a, suka sa masa tufafi masu kyau, sa'annan ya sake aika Yesu zuwa wurin Bilatus.
12 And Herod and Pilate became friends that very day, for before that there had been ill-will between them.
Sai Hirudus da Bilatus suka zama abokai a wannan rana (da ma su abokai gaba ne).
13 So Pilate summoned the Chief Priests, and the leading men, and the people,
Bilatus ya kira manyan firistoci tare da masu mulki da kuma taron jama'ar,
14 and said to them: “You brought this man before me charged with misleading the people; and yet, for my part, though I examined him before you, I did not find this man to blame for any of the things of which you accuse him;
sai ya ce masu, “Kun kawo mani wannan mutum kamar wanda yake jagorar mutane ga munanan ayyuka, ku kuma gani, Ni, na tuhume shi a gabanku, ban sami ko kuskure daya daga mutumin nan game da abinda ku ke zarginsa da shi ba.
15 nor did Herod either; for he has sent him back to us. And, as a fact, he has not done anything deserving death;
Babu, ko Hirudus ma, ya sake komar mana da shi, kun gani, babu wani abu wanda ya yi da ya cancanci mutuwa,
16 so I shall have him scourged, and then release him.”
saboda haka zan yi masa horo sa'annan in sake shi.”
[Ya zama dole Bilatus ya sakar wa Yahudawa wani daurarre guda daya lokacin idin.]
18 But they began to shout as one man: “Kill this fellow, but release Barabbas for us.”
Amma dukansu suka yi ihu tare, cewa, “A tafi da wannan mutumin, sai a sako mana Barabbas!”
19 (Barabbas was a man who had been put in prison for a riot that had broken out in the city and for murder.)
Barabbas mutum ne wanda aka sa a cikin kurkuku saboda wani tada hankali a cikin birni da kuma kisankai.
20 Pilate, however, wanting to release Jesus, called to them again;
Bilatus ya sake yi masu magana, yana so ya saki Yesu.
21 but they kept calling out: “Crucify, crucify him!”
Amma suka yi ihu, cewa, “A giciye shi, a giciye shi.”
22 “Why, what harm has this man done?” Pilate said to them for the third time. “I have found nothing in him for which he could be condemned to death. So I will have him scourged, and then release him.”
Sai ya sake ce masu sau na uku, “Don me, wace magunta wannan mutum ya yi? Ban sami wani abu da ya isa sanadin mutuwa game da shi ba. Saboda haka bayan na hore shi, zan sake shi.”
23 But they persisted in loudly demanding his crucifixion; and their clamour gained the day.
Amma suka nace da murya mai karfi, suna so a giciye shi, sai muryarsu ta rinjayi Bilatus.
24 Pilate decided that their demand should be granted.
Sai Bilatus ya yarda ya yi masu bisa ga abin da suke so.
25 He released the man who had been put in prison for riot and murder, as they demanded, and gave Jesus up to be dealt with as they pleased.
Ya sako masu wanda suka tambaya ya ba su wanda aka sa a kurkuku domin tada hankali da kuma kisankai. Amma ya ba da Yesu bisa nufinsu.
26 And, as they were leading Jesus away, they laid hold of Simon from Cyrene, who was on his way in from the country, and they put the cross on his shoulders, for him to carry it behind Jesus.
Da suka tafi da shi, sai suka kama wani mai suna siman Bakurane, yana zuwa daga karkara, sai suka daura masa giciyen ya dauka, yana biye da Yesu.
27 There was a great crowd of people following him, many being women who were beating their breasts and wailing for him.
Babban taron jama'a, da na mata da suke makoki da kuka dominsa, suna binsa.
28 So Jesus turned and said to them: “Women of Jerusalem, do not weep for me, but weep for yourselves and for your children.
Amma da ya juya wurinsu, Yesu yace, “Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka domina, amma ku yi kuka domin kanku da 'ya'yanku.
29 A time, I tell you, is coming, when it will be said — ‘Happy are the women who are barren, and those who have never borne children or nursed them!’
Gama ku gani, kwanaki suna zuwa da za su ce, 'Albarka ta tabbata ga bakararru da wadanda basu taba haihuwa ba da kuma wadanda ba a taba shan mamansu ba.'
30 At that time people will begin to say to the mountains ‘Fall on us,’ and to the hills ‘Cover us.’
Sa'annan za su fara ce wa duwatsu, 'Ku fado bisanmu,' da tuddai ma, 'Ku rufe mu.'
31 If what you see is done while the tree is green, what will happen when it is dry?”
Gama idan sun yi wadannan abubuwan lokacin da itace yana danye, me zai faru sa'adda ya bushe?”
32 There were two others also, criminals, led out to be executed with Jesus.
Aka kai wadansu mutum biyu masu laifi, domin a kashe shi tare da su.
33 When they had reached the place called ‘The Skull,’ there they crucified Jesus and the criminals, one on the right, and one on the left.
Sa'adda suka zo wurin da a ke kira kwalluwa, nan suka giciye shi da barayin, daya daga hannun damansa dayan kuma daga hannun hagu.
34 Then Jesus said: “Father, forgive them; they do not know what they are doing.” His clothes they divided among them by casting lots.
Yesu yace, “Uba, ka yafe masu, gama basu san abin da suke yi ba.” Sai suka jefa kuri'a, suka rarraba tufafinsa.
35 Meanwhile the people stood looking on. Even the leading men said with a sneer: “He saved others, let him save himself, if he is God’s Christ, his Chosen One.”
Mutane sun tsaya suna kallo sa'annan masu mulki suna ta yin masa ba'a, cewa, “Ya ceci wadansu. Bari ya ceci kansa, idan shine Almasihu na Allah, zababben nan.”
36 The soldiers, too, came up in mockery, bringing him common wine,
Sojojin ma suka yi masa dariya, suna zuwa wurinsa, suna mika masa ruwan tsami,
37 and saying as they did so: “If you are the King of the Jews, save yourself.”
suna cewa, “Idan kai Sarkin Yahudawa ne, ceci kanka.”
38 Above him were the words — ‘THIS IS THE KING OF THE JEWS.’
Akwai wata alama bisansa, “Wannan shine Sarkin Yahudawa.”
39 One of the criminals who were hanging beside Jesus railed at him. “Are not you the Christ? Save yourself and us,” he said.
Daya daga cikin barayi wanda aka giciye, ya zage shi, cewa, “Ba kai ne Almasihu ba? Ka ceci kanka da mu.”
40 But the other rebuked him. “Have not you,” he said, “any fear of God, now that you are under the same sentence?
Amma dayan ya amsa, ya tsauta masa cewa, “Ba ka tsoron Allah, da yake shari'arka daya ne da nasa?
41 And we justly so, for we are only reaping our deserts, but this man has not done anything wrong.
Mu kam an yi ma na daidai, gama mun samu bisa ga abin da muka yi. Amma wannan mutum bai yi wani abu mara kyau ba.”
42 Jesus,” he went on, “do not forget me when you have come to your Kingdom.”
Sai ya kara, “Yesu, ka tuna da ni sa'adda ka shiga mulkinka.”
43 And Jesus answered: “I tell you, this very day you shall be with me in Paradise.”
Yesu ya ce masa, “Gaskiya ina ce maka, yau za ka kasance tare da ni a firdausi.”
44 It was nearly mid-day, when a darkness came over the whole country, lasting till three in the afternoon,
Anan nan a wajen sa'a na shida, sai duhu ya mamaye kasar duka har zuwa sa'a na tara
45 the sun being eclipsed; and the Temple curtain was torn down the middle.
sa'adda rana ya fadi. Sai labulen haikalin ya rabu a tsakiya zuwa kasa.
46 Then Jesus, with a loud cry, said: “Father, into thy hands I commit my spirit.” And with these words he expired.
Da kuka da murya mai karfi, Yesu yace, “Uba, na mika Ruhu na a hannunka.” Bayan da ya fadi wannan, sai ya mutu.
47 The Roman Captain, on seeing what had happened, praised God, exclaiming: “This must have been a good man!”
Sa'adda jarumin ya ga abin da ya faru, ya daukaka Allah, cewa, “Lallai wannan mutumin mai adalci ne.”
48 All the people who had collected to see the sight watched what occurred, and then went home beating their breasts.
Sa'adda dukan taro mai yawa wadanda suka zo tare domin su shaida da idanunsu suka ga abubuwan da suka faru, suka koma suna bugan kirjinsu.
49 All the friends of Jesus had been standing at a distance, with the women who accompanied him from Galilee, watching all this.
Amma duk idon sani, da kuma matan da suka bi shi tun daga Galili, suka tsaya daga nesa, suna duban wadannan abubuwa.
50 Now there was a man of the name of Joseph, who was a member of the Council, and who bore a good and upright character.
Ga shi kuwa, wani mutum mai suna Yusufu, shi dan majalisa ne, nagari ne kuma mutum mai adalci ne
51 (This man had not assented to the decision and action of the Council.) He belonged to Ramah, a town in Judea, and lived in expectation of the Kingdom of God.
(bai yarda da shawarar da kuma abin da suka aikata ba), daga Arimatiya a kasar Yahudiya, wanda yake jiran mulkin Allah.
52 He now went to see Pilate, and asked for the body of Jesus;
Wannan mutum, ya sami Bilatus, ya tambaya a bashi jikin Yesu.
53 and, when he had taken it down, he wrapped it in a linen sheet, and laid him in a tomb cut out of stone, in which no one had yet been buried.
Ya saukar da shi kasa, sai ya nade shi cikin likafani na linin mai kyau, ya kwantar da shi cikin kabari da aka sassaka shi daga dutse, inda ba a taba binne wani ba.
54 It was the Preparation Day, and just before the Sabbath began.
Ranar kuwa, ranar shiri ce, Asabaci kuma ta kusato.
55 The women who had accompanied Jesus from Galilee followed, and saw the tomb and how the body of Jesus was laid,
Matan da suka taho da shi tun daga Galili, suka biyo baya, su ga kabarin da inda aka ajiye shi.
56 and then went home, and prepared spices and perfumes.
Suka koma, sai suka shirya kayan kamshi da mai. Suka kuma huta a ranar Asabaci bisa ga doka.

< Luke 23 >