< Psalms 139 >

1 To the Chief Musician, David’s. A Melody. O Yahweh! thou hast searched me, and observed:
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
2 Thou, hast observed my downsitting and mine uprising, Thou hast given heed to my desire, from afar:
Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
3 My path and my couch, hast thou examined, and, all my ways, thou well knowest.
Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
4 Surely there hath not been a word on my tongue, [but] behold! O Yahweh, thou hast observed it on every side.
Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
5 Behind and before, hast thou shut me in, and hast laid upon me thy hand: —
Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
6 Knowledge, too wonderful, for me! high, I cannot attain to it!
Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
7 Whither can I go from thy spirit? or whither, from thy face, can I flee?
Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
8 If I ascend the heavens, there, thou art! If I spread out hades as my couch, behold thee! (Sheol h7585)
In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
9 If I mount the wings of the dawn, settle down in the region beyond the sea,
In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
10 Even there, thy hand shall lead me, and thy right hand shall hold me.
can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
11 If I say, Surely, darkness, shall cover me! then, night, is light about me.
In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
12 Even darkness, will not conceal from thee, —but, night, like day, will shine, So is the darkness, as the light!
duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
13 For, thou, didst possess thyself of my reins, thou didst weave me together in the womb of my mother.
Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
14 I thank thee, in that fearfully was my being distinguished, Wonderful are thy works, and, mine own soul, is observing [them] intently!
Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
15 My substance was not hid from thee, —when I was made in secret, when I was skilfully figured in the lower parts of the earth.
Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
16 Mine unfinished substance, thine eyes beheld, and, in thy book, all the parts thereof were written, —the days they should be fashioned! while yet there was not one among them.
Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
17 To me, then, how precious have thy desires become, O GOD! How numerous, the heads of them!
Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
18 I would recount them! Beyond the sands, they multiply, I rouse myself—and am still with thee.
A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
19 Wilt thou not, O GOD, slay the lawless one? Therefore, ye men of bloodshed, depart from me!
Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
20 For they speak of thee wickedly, Thy foes lift up [their hand] unto falsehood.
Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
21 Do I not hate, them who hate thee, O Yahweh? And loathe, them who rise up against thee?
Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
22 With completeness of hatred, I hate them, As enemies, have they become to me.
Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
23 Search me, O GOD, and observe my heart, Try me, and observe my cares;
Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
24 And see if there be any idol-way in me, and lead me in a way age-abiding.
Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.

< Psalms 139 >