< Judges 5 >

1 Then sang Deborah with Barak the son of Abino'am on that day, saying,
A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
2 When depravity had broken out in Israel, then did the people offer themselves willingly; [therefore] praise ye the Lord.
“Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
3 Hear, O kings; give ear, O princes; I—unto the Lord will I sing; I will sing praise to the Lord, the God of Israel.
“Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
4 Lord, at thy going forth out of Seir, at thy marching along out of the field of Edom, the earth trembled, also the heavens dropped, also the clouds dropped water.
“Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
5 The mountains melted away because of the presence of the Lord, yonder Sinai, because of the presence of the Lord, the God of Israel.
Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
6 In the days of Shamgar the son of 'Anath, in the days of Ja'el, the highways were unoccupied, and those who travelled on roads walked through crooked by-paths.
“A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
7 Desolate were the open towns in Israel, they were desolate, until that I arose, Deborah, that I arose a mother in Israel.
Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
8 They chose new gods, then was there war in the gates: was there a shield seen or a spear among forty thousand in Israel?
Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
9 My heart [belongeth] to the governors of Israel, that offered themselves willingly among the people: praise ye the Lord.
Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
10 Ye that ride on white asses, ye that sit in judgment, and ye who walk on the way, utter praise!
“Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
11 [Urged on] by the voice of those who divide [the flocks] between the watering wells, there shall they rehearse the benefits of the Lord, the benefits toward his open towns in Israel; [for] now go down [again] to the gates the people of the Lord.
da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
12 Awake, awake, Deborah! awake, awake, utter a song! up, Barak, and lead away thy captives, son of Abino'am.
‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
13 Then obtained dominion a few that had escaped for the nobles among the people—the Lord gave me dominion over the mighty.
“Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
14 They whose root is out of Ephraim were against 'Amalek; after thee, Benjamin, with thy armies; out of Machir came down lawgivers, and out of Zebulun they that handle the pen of the writer.
Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
15 And the princes of Issachar were with Deborah; yea Issachar, the support of Barak; into the valley he hastened down in his train; [but] at the streams of Reuben there were great thoughts of heart.
’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
16 Why didst thou sit among the sheepfolds to hear the bleatings of the flocks? At the streams of Reuben there were great searchings of heart.
Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
17 Gil'ad abode beyond the Jordan; and Dan—why would he tarry in ships? Asher remained on the seashore, and abode near his bays.
Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
18 Zebulun is a people that jeoparded its life unto death, and Naphtali—on the high places of the [battle] field.
Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
19 There came kings, [and] fought, then fought the kings of Canaan, in Ta'anach by the waters of Megiddo: gain of money they took not away.
“Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
20 From heaven they fought—the stars in their courses fought against Sissera.
Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
21 The stream of Kishon swept them away, that ancient stream, the stream of Kishon: step along, O my soul, in victorious strength.
Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
22 Then were crushed the hoofs of the horses, through the prancings, the prancings of their mighty ones.
Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
23 Curse ye Meroz, saith the messenger of the Lord, yea, curse ye bitterly its inhabitants; because they came not to the help of the Lord, to the help of the Lord among the mighty.
Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
24 Blessed above [other] women shall be Ja'el the wife of Cheber the Kenite, above [other] women [dwelling] in the tent may she be blessed.
“Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
25 Water he asked, milk she gave [him]: in a lordly dish she brought him cream.
Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
26 Her hand she put forth to the nail, and her right hand to the laborious workmen's hammer; and she hammered Sissera, she struck his head, and crushed and smote through his temple.
Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
27 Between her feet he bent, he fell, he lay; between her feet he bent, he fell: where he had bent, there he fell down, bereft of life.
A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
28 Out of the window looked and moaned the mother of Sissera, through the lattice, Why tarrieth his chariot so long in coming? why lag the wheels of his chariot?
“Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
29 The wise among her ladies answered her, she also returned a reply to herself.
Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
30 Will they not find, —divide booty? one maiden, two maidens for every man, a booty of colored garments for Sissera, a booty of colored embroidered garments, colored, double-worked garments round the necks of the captives!
‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
31 Thus may perish all thy enemies, O Lord; but may those that love him be as the rising of the sun in his might. And the land had rest forty years.
“Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.

< Judges 5 >