< Jeremiah 1 >

1 The words of Jeremiah the son of Chilkiyahu, one of the priests that were in 'Anathoth in the land of Benjamin;
Kalmomin Irmiya ɗan Hilkiya, ɗaya daga cikin firistoci a Anatot a yankin Benyamin.
2 To whom the word of the Lord came in the days of Josiah the son of Amon the king of Judah, in the thirteenth year of his reign,
Maganar Ubangiji ta zo gare shi a shekara ta goma sha uku ta sarautar Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda,
3 And who continued [prophet] in the days of Jehoyakim the son of Josiah the king of Judah, until the end of the eleventh year of Zedekiah the son of Josiah the king of Judah, until the carrying away into exile of Jerusalem in the fifth month.
da kuma a zamanin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, har zuwa watan biyar na shekara goma sha ɗaya na Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, sa’ad da aka kai mutanen Urushalima zaman bauta.
4 And the word of the Lord came unto me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
5 Before yet I had formed thee in thy mother's body I knew thee; and before thou wast yet come forth out of the womb I sanctified thee: a prophet unto the nations did I ordain thee.
“Kafin in siffanta ka a cikin ciki na san ka, kafin a haife ka, na keɓe ka; na naɗa ka ka zama annabi ga al’ummai.”
6 And I said, Ah, Lord Eternal! behold, I know not how to speak; for I am [but] a lad.
Sai na ce, “Kayya, Ubangiji Mai Iko Duka, ban iya magana ba; ni ɗan yaro ne kawai.”
7 And the Lord said unto me, Say not, I am [but] a lad; but to whomsoever I may send thee shalt thou go, and whatsoever I may command thee shalt thou speak.
Amma Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ce, ‘Ni ɗan yaro ne kawai.’ Dole ka je wurin kowane mutumin da na aike ka ka kuma faɗa abin da na umarce ka.
8 Be not afraid because of them; for I am with thee to deliver thee, saith the Lord.
Kada ka ji tsoronsu, gama ina tare da kai kuma zan kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
9 And the Lord stretched forth his hand, and touched [me] therewith on my mouth; and the Lord said unto me, Behold, I have put my words in thy mouth.
Sai Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina ya ce mini, “Yanzu na sa kalmomina a bakinka.
10 See, I have appointed thee this day over the nations and over the kingdoms, to root out, and to pull down, and to destroy, and to throw down: to build up, and to plant.
Duba, yau na naɗa ka a kan al’ummai da mulkoki don ka tumɓuke ka kuma rusar, ka hallaka ka kuma kakkaɓe, ka gina ka kuma shuka.”
11 And the word of the Lord came unto me, saying, What seest thou, Jeremiah? And I said, A staff of all almond-tree do I see.
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa, “Me ka gani, Irmiya?” Sai na amsa na ce, “Na ga reshen itacen almon.”
12 And the Lord said unto me, Thou hast well seen; for I am watching over my word to perform it.
Ubangiji ya ce mini, “Daidai ne ka gani, gama ina lura in ga cewa maganata ta cika.”
13 And the word of the Lord came unto me the second time, saying, What seest thou? And I said, A seething pot do I see; and the front thereof is turned from the north.
Maganar Ubangiji ta sāke zo mini cewa, “Me ka gani?” Na amsa na ce, “Na ga tukunya tana tafasa, tana juyewa daga arewa.”
14 And the Lord said unto me, Out of the north shall the evil break forth over all the inhabitants of the land,
Ubangiji ya ce mini, “Daga arewa za a zubo masifa a kan dukan mazaunan ƙasar.
15 For, lo, I will call unto all the families of the kingdoms of the north, saith the Lord; and they shall come, and they shall set every one his throne at the entrance of the gates of Jerusalem, and upon all its walls round about, and upon [those of] all the cities of Judah.
Ina shirin kiran dukan mutanen masarautar arewanci,” in ji Ubangiji. “Sarakunansu za su zo su kafa kursiyoyinsu a mashigin ƙofofin Urushalima; za su zo su kewaye dukan katangarta su kewaye dukan garuruwan Yahuda.
16 And I will call them to account touching all their wickedness, in that they have forsaken me, and have burnt incense unto other gods, and have bowed down unto the works of their own hands.
Zan furta hukunci a kan mutanena saboda muguntarsu na yashe ni, suna ƙona turare ga waɗansu alloli suna kuma bauta wa abin da hannuwansu suka yi.
17 But do thou gird up thy loins, and arise, and speak unto them all that I may command thee; be not discouraged because of them, lest I humble thee before them.
“Ka kintsa kanka! Ka tashi tsaye ka faɗa musu abin da na umarce ka. Kada su firgita ka, in ba haka ba zan firgita ka a gabansu.
18 But I, behold, I have made of thee this day a fortified city, and an iron pillar, and brazen walls over the whole land, against the kings of Judah, against its princes, against its priests, and against the people of the land.
Yau na mai da kai birni mai katanga, ginshiƙin ƙarfe da bangon tagulla don ka tsaya gāba da dukan ƙasar, ya kuma yi gāba da sarakunan Yahuda da fadawan, da firistoci da kuma mutanenta.
19 And [although] they fight against thee, they shall not prevail against thee; for with thee am I saith the Lord, to deliver thee.
Za su yi yaƙi da kai amma ba za su ci nasara a kanka ba, gama ina tare da kai, zan kuma kiyaye ka,” in ji Ubangiji.

< Jeremiah 1 >