< Ezekiel 28 >
1 And the word of the LORD came unto me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 'Son of man, say unto the prince of Tyre: Thus saith the Lord GOD: Because thy heart is lifted up, and thou hast said: I am a god, I sit in the seat of God, in the heart of the seas; yet thou art man, and not God, though thou didst set thy heart as the heart of God —
“Ɗan mutum, ka faɗa wa mai mulkin Taya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Cikin alfarmar zuciyarka ka ce, “Ni allah ne; ina zama a kan kursiyin allah a tsakiyar tekuna.” Amma kai mutum ne ba allah ba, ko da yake ka ɗauka kana da hikima kamar allah.
3 Behold, thou art wiser than Daniel! there is no secret that they can hide from thee!
Ka fi Daniyel hikima ne? Ba asirin da yake ɓoye a gare ka?
4 By thy wisdom and by thy discernment thou hast gotten thee riches, and hast gotten gold and silver into thy treasures;
Ta wurin hikimarka da ganewarka ka sami dukiya wa kanka ka kuma tara zinariya da azurfa cikin wuraren ajiyarka.
5 In thy great wisdom by thy traffic hast thou increased thy riches, and thy heart is lifted up because of thy riches —
Ta wurin dabararka mai girma cikin kasuwanci ka ƙara dukiyarka, kuma saboda dukiyarka zuciyarka ta cika da alfarma.
6 Therefore thus saith the Lord GOD: Because thou hast set thy heart as the heart of God;
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Domin ka ɗauka kai mai hikima ne, mai hikima kamar allah,
7 Therefore, behold, I will bring strangers upon thee, the terrible of the nations; and they shall draw their swords against the beauty of thy wisdom, and they shall defile thy brightness.
zan kawo baƙi a kanka, waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al’ummai; za su zāre takubansu a kan kyakkyawar hikimarka su kuma ɓarke darajarka mai walƙiya.
8 They shall bring thee down to the pit; and thou shalt die the deaths of them that are slain, in the heart of the seas.
Za su jefar da kai cikin rami, za ka kuwa yi muguwar mutuwa a tsakiyar tekuna.
9 Wilt thou yet say before him that slayeth thee: I am God? But thou art man, and not God, in the hand of them that defile thee.
Za ka iya ce yanzu, “Ni allah ne,” a gaban waɗanda suka kashe ka? Za ka zama mutum kurum, ba allah ba, a hannuwan waɗanda suka kashe ka.
10 Thou shalt die the deaths of the uncircumcised by the hand of strangers; for I have spoken, saith the Lord GOD.'
Za ka yi mutuwar marar kaciya a hannuwan baƙi. Na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
11 Moreover the word of the LORD came unto me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
12 'Son of man, take up a lamentation for the king of Tyre, and say unto him: Thus saith the Lord GOD: Thou seal most accurate, full of wisdom, and perfect in beauty,
“Ɗan mutum, ka yi makoki domin sarkin Taya ka kuma ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka kasance hatimin cikakke, cike da hikima da cikakke a kyau.
13 thou wast in Eden the garden of God; every precious stone was thy covering, the carnelian, the topaz, and the emerald, the beryl, the onyx, and the jasper, the sapphire, the carbuncle, and the smaragd, and gold; the workmanship of thy settings and of thy sockets was in thee, in the day that thou wast created they were prepared.
Ka kasance a Eden, a lambun Allah; aka yi maka ado da kowane dutse mai daraja, yakutu, tofaz, da zumurrudu, kirisolit, onis da yasfa, saffaya, turkuwoyis da beril. Tsare-tsare da shirye-shiryenka an yi su da zinariya ne; a ranar da aka halicce ka an shirya su.
14 Thou wast the far-covering cherub; and I set thee, so that thou wast upon the holy mountain of God; thou hast walked up and down in the midst of stones of fire.
An shafe ka kamar kerub mai tsaro, gama haka na naɗa ka. Kana a tsattsarkan dutsen Allah; ka yi tafiya a tsakiyar duwatsun wuta.
15 Thou wast perfect in thy ways from the day that thou wast created, till unrighteousness was found in thee.
Ka kasance marar laifi cikin dukan hanyoyinka daga ranar da aka halicce ka sai da aka sami mugunta a cikinka.
16 By the multitude of thy traffic they filled the midst of thee with violence, and thou hast sinned; therefore have I cast thee as profane out of the mountain of God; and I have destroyed thee, O covering cherub, from the midst of the stones of fire.
Ta wurin yawan kasuwancinka ka cika da rikici, ka kuma yi zunubi. Saboda haka na kore ka da kunya daga dutsen Allah, na kore ka, ya kerub mai tsaro, daga cikin duwatsun wuta.
17 Thy heart was lifted up because of thy beauty, thou hast corrupted thy wisdom by reason of thy brightness; I have cast thee to the ground, I have laid thee before kings, that they may gaze upon thee.
Zuciyarka ta cika da alfarma saboda kyanka, ka kuma lalace hikimarka saboda darajarka. Saboda haka na jefar da kai zuwa ƙasa; na sa ka zama abin kallo a gaban sarakuna.
18 By the multitude of thine iniquities, in the unrighteousness of thy traffic, thou hast profaned thy sanctuaries; therefore have I brought forth a fire from the midst of thee, it hath devoured thee, and I have turned thee to ashes upon the earth in the sight of all them that behold thee.
Ta wurin yawan zunubanka da kasuwancinka na cuta ka ƙazantar da wuri mai tsarkinka. Saboda haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka, na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suke kallonka.
19 All they that know thee among the peoples shall be appalled at thee; thou art become a terror, and thou shalt never be any more.'
Dukan al’umman da suka san ka sun giggice saboda masifar da ta auko maka; ka zo ga mummunar ƙarshe ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.’”
20 And the word of the LORD came unto me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
21 'Son of man, set thy face toward Zidon, and prophesy against it,
“Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon; ka yi annabci a kanta
22 and say: Thus saith the Lord GOD: Behold, I am against thee, O Zidon, and I will be glorified in the midst of thee; and they shall know that I am the LORD, when I shall have executed judgments in her, and shall be sanctified in her.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da ke, ya Sidon, zan sami ɗaukaka a cikinki. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na zartar da hukunci a kanta na kuma nuna kaina mai tsarki a cikinta.
23 For I will send into her pestilence and blood in her streets; and the wounded shall fall in the midst of her by the sword upon her on every side; and they shall know that I am the LORD.
Zan aika da annoba a kanta in kuma sa jini ya zuba a titunanta. Kisassu za su fāɗi a cikinta, da takobi yana gāba da ita a kowane gefe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.
24 And there shall be no more a pricking brier unto the house of Israel, nor a piercing thorn of any that are round about them, that did have them in disdain; and they shall know that I am the Lord GOD.
“‘Mutanen Isra’ila ba za su ƙara kasance da mugayen maƙwabta waɗanda za su zama sarƙaƙƙiya masu zafi da ƙaya mai tsini ba. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
25 Thus saith the Lord GOD: When I shall have gathered the house of Israel from the peoples among whom they are scattered, and shall be sanctified in them in the sight of the nations, then shall they dwell in their own land which I gave to My servant Jacob.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na tattara mutanen Isra’ila daga al’ummai inda suke a warwatse, zan nuna kaina mai tsarki a cikinsu a idon al’ummai. Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu, wadda na ba wa bawana Yaƙub.
26 And they shall dwell safely therein, and shall build houses, and plant vineyards; yea, they shall dwell safely; when I have executed judgments upon all those that have them in disdain round about them; and they shall know that I am the LORD their God.'
Za su zauna a can lafiya su kuma gina gidaje su nome gonakin inabi; za su zauna lafiya sa’ad da zan zartar da hukunci a kan dukan maƙwabtansu da suka wulaƙanta su. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.’”