< Romans 1 >

1 Paul a seruant of Iesus Christ called to be an Apostle, put apart to preache the Gospel of God,
Bulus, bawan Kiristi Yesu, kirayaye don yă zama manzo, keɓaɓɓe kuma domin bisharar Allah.
2 (Which he had promised afore by his Prophetes in the holy Scriptures)
Bisharar da Allah ya yi alkawari tuntuni ta bakin annabawansa a cikin Nassosi Masu Tsarki
3 Concerning his Sonne Iesus Christ our Lord (which was made of the seede of Dauid according to the flesh,
game da Ɗansa. Wanda bisa ga mutuntakarsa, zuriyar Dawuda ne.
4 And declared mightily to be the Sonne of God, touching the Spirit of sanctification by the resurrection from the dead)
Wanda bisa ga Ruhun tsarki, an shaida shi da iko cewa shi Ɗan Allah ne ta wurin tashinsa daga matattu. Wannan bishara kuwa game da Yesu Kiristi Ubangijinmu ne.
5 By whom we haue receiued grace and Apostleship (that obedience might be giuen vnto ye faith) for his Name among al ye Gentiles,
Ta wurinsa da kuma saboda sunansa, muka sami alheri muka kuma zama manzanni don mu kira mutane daga cikin dukan Al’ummai zuwa ga biyayyar da take zuwa daga bangaskiya.
6 Among whom ye be also the called of Iesus Christ:
Ku ma kuna cikin waɗanda aka kira ku zama na Yesu Kiristi.
7 To all you that be at Rome beloued of God, called to be Saints: Grace be with you, and peace from God our Father, and from the Lord Iesus Christ.
Wannan wasiƙa ce zuwa ga dukanku da kuke a Roma waɗanda Allah yake ƙauna, waɗanda kuma ya kira domin su zama tsarkaka. Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma daga Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
8 First I thanke my God through Iesus Christ for you all, because your faith is published throughout the whole world.
Da farko, ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Kiristi saboda ku duka, gama ana ba da labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya.
9 For God is my witnesse (whom I serue in my spirit in the Gospel of his Sonne) that without ceasing I make mention of you
Allah, wanda nake bauta wa da dukan zuciyata cikin wa’azin bisharar Ɗansa, shi ne shaidata a kan yadda kullum ina tunawa da ku
10 Alwayes in my prayers, beseeching that by some meanes, one time or other I might haue a prosperous iourney by the will of God, to come vnto you.
cikin addu’o’ina a kowane lokaci; ina kuma addu’a cewa a ƙarshe in Allah ya yarda hanya za tă buɗe mini in zo wurinku.
11 For I long to see you, that I might bestowe among you some spirituall gift, that you might be strengthened:
Ina marmarin ganinku don in ba ku wata baiwar ruhaniya, don ku yi ƙarfi
12 That is, that I might be comforted together with you, through our mutuall faith, both yours and mine.
wato, don ni da ku mu ƙarfafa juna ta wurin bangaskiyarmu.
13 Now my brethren, I would that ye should not be ignorant, how that I haue oftentimes purposed to come vnto you (but haue bene let hitherto) that I might haue some fruite also among you, as I haue among the other Gentiles.
Ina so ku sani’yan’uwa cewa na yi shirin zuwa wurinku sau da dama (amma aka hana ni yin haka sai yanzu). Na so in zo domin in sami mutane wa Kiristi a cikinku, kamar yadda na yi a cikin sauran Al’ummai.
14 I am detter both to the Grecians, and to the Barbarians, both to the wise men and vnto the vnwise.
Ina da hakki ga Hellenawa da waɗanda ba Hellenawa ba, ga masu hikima da kuma marasa azanci.
15 Therefore, as much as in me is, I am readie to preach ye Gospel to you also that are at Rome.
Shi ya sa na yi himma sosai in yi muku wa’azin bishara ku ma da kuke a Roma.
16 For I am not ashamed of the Gospel of Christ: for it is the power of God vnto saluation to euery one that beleeueth, to the Iewe first, and also to the Grecian.
Ba na jin kunyar bishara, gama ita ikon Allah ne domin ceton kowa da ya gaskata, da farko ga Yahudawa, sa’an nan ga Al’ummai.
17 For by it the righteousnesse of God is reueiled from faith to faith: as it is written, The iust shall liue by faith.
Gama a cikin bishara an bayyana adalci daga Allah wanda yake ta wurin bangaskiya daga farko zuwa ƙarshe, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
18 For the wrath of God is reueiled from heauen against all vngodlinesse, and vnrighteousnesse of men, which withhold the trueth in vnrighteousnesse.
Ana bayyana fushin Allah daga sama a kan dukan rashin sanin Allah da kuma muguntar mutanen da suke danne gaskiya ta wurin muguntarsu,
19 Forasmuch as that, which may be knowe of God, is manifest in them: for God hath shewed it vnto them.
gama abin da ana iya sani game da Allah a bayyane yake a gare su, domin Allah ya bayyana musu shi.
20 For the inuisible things of him, that is, his eternal power and Godhead, are seene by ye creation of the worlde, being considered in his workes, to the intent that they should be without excuse: (aïdios g126)
Gama tun halittar duniya halayen Allah marar ganuwa, madawwamin ikonsa da kuma allahntakarsa, ana iya ganinsu sarai, ana fahimtarsu ta wurin abubuwan da Allah ya halitta, domin kada mutane su sami wata hujja. (aïdios g126)
21 Because that when they knewe God, they glorified him not as God, neither were thankefull, but became vaine in their thoughtes, and their foolish heart was full of darkenesse.
Gama ko da yake sun san Allah, ba su ɗaukaka shi a matsayin Allah ko su gode masa ba, sai dai tunaninsu ya zama banza, zukatansu masu wauta kuma suka duhunta.
22 When they professed themselues to be wise, they became fooles.
Ko da yake sun ɗauka su masu hikima ne, sai suka zama wawaye,
23 For they turned the glorie of the incorruptible God to the similitude of the image of a corruptible man, and of birdes, and foure footed beastes, and of creeping things.
suka kuma yi musayar ɗaukakar Allah marar mutuwa da siffofin da aka ƙera su yi kama da mutum mai mutuwa da tsuntsaye da dabbobi da kuma halittu masu ja da ciki.
24 Wherefore also God gaue them vp to their hearts lusts, vnto vncleannesse, to defile their owne bodies betweene themselues:
Saboda haka Allah ya yashe su ga mugayen sha’awace-sha’awacen zukatansu ga fasikanci don a ƙasƙantar da jikunansu ga yin abin kunya.
25 Which turned the trueth of God vnto a lie, and worshipped and serued the creature, forsaking the Creator, which is blessed for euer, Amen. (aiōn g165)
Sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, suka kuma yi wa abubuwan da aka halitta sujada suna bauta musu a maimakon Mahalicci, wanda ake yabo har abada. Amin. (aiōn g165)
26 For this cause God gaue them vp vnto vile affections: for euen their women did change the naturall vse into that which is against nature.
Saboda wannan, Allah ya yashe su ga sha’awace-sha’awacensu masu banƙyama. Har matansu suka sauya daga haɗuwar mace da miji wadda ita ce daidai bisa ga halitta zuwa haɗuwa da’yan’uwansu mata wadda ba daidai ba.
27 And likewise also the men left the naturall vse of the woman, and burned in their lust one toward another, and man with man wrought filthinesse, and receiued in themselues such recompence of their errour, as was meete.
Haka ma maza suka bar al’adar kwana da mata suka tunzura cikin sha’awar kwana da juna, abin da ba daidai ba bisa ga halitta. Maza suka aikata rashin kunya da waɗansu maza, suka jawo wa kansu sakamako daidai da bauɗewarsu.
28 For as they regarded not to acknowledge God, euen so God deliuered them vp vnto a reprobate minde, to doe those things which are not conuenient,
Da yake ba su yi tunani cewa ya dace su riƙe sanin Allah da suke da shi ba, sai ya yashe su ga tunanin banza da wofi, su aikata abin da bai kamata a yi ba.
29 Being full of all vnrighteousnesse, fornication, wickednes, couetousnes, maliciousnes, full of enuie, of murder, of debate, of deceit, taking all things in the euill part, whisperers,
Sun cika da kowace irin ƙeta, mugunta, kwaɗayi, da tunanin banza da wofi. Suka kuma cika da kishi, kisankai, faɗa, ruɗu, da kuma riƙo a zuci. Su masu gulma ne,
30 Backbiters, haters of God, doers of wrong, proude, boasters, inuenters of euil things, disobedient to parents,
da masu ɓata suna, masu ƙin Allah, masu rashin kunya, masu girman kai, masu rigima; sukan ƙaga hanyoyin yin mugunta; suna rashin biyayya ga iyayensu;
31 without vnderstanding, couenant breakers, without naturall affection, such as can neuer be appeased, mercilesse.
su marasa hankali ne, marasa bangaskiya, marasa ƙauna, marasa tausayi.
32 Which men, though they knew ye Lawe of God, how that they which comit such things are worthie of death, yet not onely do the same, but also fauour them that doe them.
Ko da yake sun san dokar adalcin Allah cewa masu aikata irin waɗannan abubuwa sun cancanci mutuwa, duk da haka ba cin gaba da aikata waɗannan abubuwa kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon bayan masu yinsu.

< Romans 1 >