< Romans 4 >
1 What shall we say then, that Abraham our father hath found concerning the flesh?
To, me za mu ce Ibrahim kakan kakanninmu ya gani game da wannan batu?
2 For if Abraham were iustified by workes, he hath wherein to reioyce, but not with God.
In fa da gaske ne Ibrahim ya sami kuɓuta ta wurin ayyuka, yana da abin da zai yin taƙama da shi ke nan, amma ba a gaban Allah ba.
3 For what saith the Scripture? Abraham beleeued God, and it was counted to him for righteousnesse.
Me Nassin ya ce? “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
4 Nowe to him that worketh, the wages is not counted by fauour, but by dette:
To, sa’ad da mutum ya yi aiki, ba a lissafta ladan aikinsa a matsayin kyauta, sai dai a matsayin hakkinsa.
5 But to him that worketh not, but beleeueth in him that iustifieth the vngodly, his faith is counted for righteousnesse.
Amma fa, game da mutumin da ba ya aiki sai dai dogara ga Allah wanda yake kuɓutar da masu mugunta, akan lissafta bangaskiyarsa a matsayin adalci ne.
6 Euen as Dauid declareth the blessednesse of the man, vnto whom God imputeth righteousnes without workes, saying,
Dawuda ya faɗi haka sa’ad da ya yi magana game da albarkar da aka yi wa mutumin da Allah ya lissafta adalci a gare shi, ba don yă yi ayyuka ba.
7 Blessed are they, whose iniquities are forgiuen, and whose sinnes are couered.
“Masu albarka ne waɗanda aka gafarta laifofinsu, waɗanda aka kuma rufe zunubansu.
8 Blessed is the man, to whom the Lord imputeth not sinne.
Mai albarka ne mutumin da Ubangiji ba zai taɓa lissafta zunubansa ba.”
9 Came this blessednesse then vpon the circumcision onely, or vpon the vncircumcision also? For we say, that faith was imputed vnto Abraham for righteousnesse.
Shin, wannan albarkar a kan masu kaciya ne kawai, ko kuwa har da marasa kaciya ma? Mun sha faɗi cewa an lissafta bangaskiyar Ibrahim adalci ne a gare shi.
10 Howe was it then imputed? when he was circumcised, or vncircumcised? not when he was cricumcised, but when he was vncircumcised.
A kan wane hali ne aka lissafta masa? Bayan da aka yi masa kaciya ne, ko kuwa kafin kaciyar? Ba bayan an yi masa kaciya ba ne, amma kafin a yi masa kaciya!
11 After, he receiued the signe of circumcision, as the seale of the righteousnesse of ye faith which he had, when he was vncircumcised, that he should be the father of all them that beleeue, not being circumcised, that righteousnesse might be imputed to them also,
Ya kuma karɓi alamar kaciya, hatimin adalcin da yake da shi ta wurin bangaskiya tun yana marar kaciya. Saboda haka fa, ya zama mahaifin dukan waɗanda suka gaskata domin su ma a lasafta su masu adalci ne, ba tare da an yi musu kaciya ba.
12 And the father of circumcision, not vnto them onely which are of the circumcision, but vnto them also that walke in the steppes of the faith of our father Abraham, which he had when he was vncircumcised.
Ya kuma zama mahaifin masu kaciya waɗanda ba kaciya kaɗai suke da ita ba amma har ma suna bin gurbin bangaskiyar da mahaifinmu Ibrahim yake da ita kafin aka yi masa kaciya.
13 For the promise that he should be the heire of the worlde, was not giuen to Abraham, or to his seede, through the Lawe, but through the righteousnesse of faith.
Ba ta wurin doka ce Ibrahim da zuriyarsa suka sami alkawarin cewa zai zama magājin duniya ba, amma sai dai ta wurin adalcin da yake zuwa ta wurin bangaskiya.
14 For if they which are of the Lawe, be heires, faith is made voide, and the promise is made of none effect.
Gama da a ce masu kiyaye doka ne magāda, ai, da bangaskiya ba ta da amfani, alkawarin kuma ya zama banza,
15 For the Lawe causeth wrath: for where no Lawe is, there is no transgression.
domin doka tana jawo fushi ne. Kuma inda babu doka babu keta umarni ke nan.
16 Therefore it is by faith, that it might come by grace, and the promise might be sure to all the seede, not to that onely which is of the Lawe: but also to that which is of the faith of Abraham, who is the father of vs all,
Saboda haka, alkawari yakan zo ta wurin bangaskiya ne, domin yă zama ta wurin alheri, don a tabbatar wa dukan zuriyar Ibrahim ba kawai ga waɗanda suke na doka ba amma har ma ga waɗanda suke na bangaskiyar Ibrahim. Shi ne kuwa mahaifinmu duka.
17 (As it is written, I haue made thee a father of many nations) euen before God whom he beleeued, who quickeneth the dead, and calleth those thinges which be not, as though they were.
Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Na mai da kai uban al’ummai masu yawa.” Shi ubanmu ne a gaban Allah, wanda a cikinsa ya gaskata, Allahn da yake ba da rai ga matattu, yake kuma kiran abubuwan da ba su kasance ba su zama kamar sun kasance.
18 Which Abraham aboue hope, beleeued vnder hope, that he should be the father of many nations: according to that which was spoken to him, So shall thy seede be.
Saɓanin dukan bege, Ibrahim cikin bege ya gaskata, haka kuwa ya zama uban al’ummai masu yawa, kamar yadda aka riga aka faɗa masa cewa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
19 And he not weake in the faith, considered not his owne bodie, which was nowe dead, being almost an hundreth yeere olde, neither the deadnes of Saraes wombe.
Ba tare da ya bar bangaskiyarsa ta yi rauni ba, ya fuskanci gaskiyan nan mai cewa jikinsa mai tsufa matacce ne, da yake yana da shekara wajen ɗari, mahaifar Saratu kuma matacciya ce.
20 Neither did he doubt of the promise of God through vnbeliefe, but was strengthened in the faith, and gaue glorie to God,
Duk da haka bai yi shakka ta wurin rashin bangaskiya game da alkawarin Allah ba, sai ma ya ƙara ƙarfafa ga bangaskiyarsa, ya kuma ɗaukaka Allah,
21 Being fully assured that he which had promised, was also able to doe it.
yana kuma da cikakken tabbaci cewa Allah yana da iko yă cika abin da ya yi alkawari.
22 And therefore it was imputed to him for righteousnesse.
Shi ya sa, “aka lissafta adalci a gare shi.”
23 Nowe it is not written for him onely, that it was imputed to him for righteousnesse,
Kalmomin nan, “aka lissafta a gare shi” ba a rubuta su saboda shi kaɗai ba ne,
24 But also for vs, to whom it shalbe imputed for righteousnesse, which beleeue in him that raised vp Iesus our Lord from the dead,
amma saboda mu ma, mu da Allah zai lissafta adalci, mu da muka ba da gaskiya gare shi da ya tashe Yesu Ubangijinmu daga matattu.
25 Who was deliuered to death for our sinnes, and is risen againe for our iustification.
An miƙa shi ga mutuwa saboda zunubanmu, aka kuma tashe shi zuwa rai saboda Allah zai same mu marasa laifi.