< Revelation 1 >
1 The Reuelation of Iesus Christ, which God gaue vnto him, to shewe vnto his seruants things which must shortly be done: which he sent, and shewed by his Angel vnto his seruant Iohn,
Wahayin Yesu Kiristi, wanda Allah ya ba shi yă nuna wa bayinsa abin da lalle zai faru nan ba da daɗewa ba. Ya bayyana shi ta wurin aiko da mala’ikansa zuwa ga bawansa Yohanna,
2 Who bare record of ye word of God, and of the testimonie of Iesus Christ, and of all things that he saw.
wanda ya shaida dukan abin da ya gani, wato, maganar Allah da kuma shaidar Yesu Kiristi.
3 Blessed is he that readeth, and they that heare the wordes of this prophecie, and keepe those things which are written therein: for the time is at hand.
Mai albarka ne wanda yake karanta waɗannan kalmomin annabci, masu albarka ne kuma waɗanda suke jinsu, suke kuma sa abin da aka rubuta a ciki a zuciya, domin lokaci ya yi kusa.
4 Iohn, to the seuen Churches which are in Asia, Grace be with you, and peace from him, Which is, and Which was, and Which is to come, and from the seuen Spirits which are before his Throne,
Daga Yohanna, Zuwa ga ikkilisiyoyi bakwai da suke a lardin Asiya. Alheri da salama gare ku daga shi wanda yake a yanzu, wanda yake a dā, da kuma wanda zai zo, da kuma daga ruhohi bakwai da suke a gaban kursiyinsa,
5 And from Iesus Christ, which is that faithful witnes, and that first begotten of the dead, and that Prince of the Kings of the earth, vnto him that loued vs, and washed vs from our sinnes in his blood,
da kuma daga Yesu Kiristi, wanda yake amintaccen shaida, ɗan farin daga tashin matattu, da kuma mai mulkin sarakunan duniya. Gare shi wanda yake ƙaunarmu wanda kuma ya’yantar da mu daga zunubanmu ta wurin jininsa,
6 And made vs Kings and Priests vnto God euen his Father, to him I say be glory, and dominion for euermore, Amen. (aiōn )
ya kuma mai da mu masarauta da firistoci don mu yi wa Allahnsa da Ubansa hidima, a gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin! Amin. (aiōn )
7 Beholde, he commeth with cloudes, and euery eye shall see him: yea, euen they which pearced him thorowe: and all kinreds of the earth shall waile before him, Euen so, Amen.
“Duba, yana zuwa cikin gizagizai, kowane ido kuwa zai gan shi, har da waɗanda suka soke shi”; dukan mutanen duniya kuwa “za su yi makoki dominsa.”
8 I am Alpha and Omega, the beginning and the ending, saith the Lord, Which is, and Which was, and Which is to come, euen the Almightie.
“Ni ne Alfa da kuma Omega,” in ji Ubangiji Allah, “wanda yake a yanzu, wanda yake a dā, da kuma wanda zai zo, Maɗaukaki.”
9 I Iohn, euen your brother, and companion in tribulation, and in the kingdome and patience of Iesus Christ, was in the yle called Patmos, for the worde of God, and for the witnessing of Iesus Christ.
Ni, Yohanna, ɗan’uwanku da kuma abokin tarayyarku cikin wahala da mulki, da kuma haƙurin jimrewa da suke namu cikin Yesu, ina can tsibirin Fatmos saboda maganar Allah da kuma saboda shaidar Yesu.
10 And I was rauished in spirit on the Lordes day, and heard behinde me a great voyce, as it had bene of a trumpet,
A Ranar Ubangiji ina cikin Ruhu, sai na ji a bayana wata babbar murya kamar ƙaho,
11 Saying, I am Alpha and Omega, that first and that last: and that which thou seest, write in a booke, and send it vnto the seuen Churches which are in Asia, vnto Ephesus, and vnto Smyrna, and vnto Pergamus, and vnto Thyatira, and vnto Sardis, and vnto Philadelphia, and vnto Laodicea.
wadda ta ce, “Rubuta a cikin naɗaɗɗen littafi abin da ka gani ka kuma aika ta zuwa ga ikkilisiyoyi bakwai, zuwa Afisa, Simirna, Fergamum, Tiyatira, Sardis, Filadelfiya, da kuma Lawodiseya.”
12 Then I turned backe to see the voyce, that spake with me: and when I was turned, I sawe seuen golden candlestickes,
Sai na juya don in ga muryar da take magana da ni. Da na juya kuwa sai na ga alkukan fitilu bakwai na zinariya.
13 And in the middes of the seuen candlestickes, one like vnto the Sonne of man, clothed with a garment downe to the feete, and girded about the pappes with a golden girdle.
A tsakiyar alkukan kuwa akwai wani “kama da ɗan mutum,” saye da rigar da ya kai har ƙafafunsa da kuma ɗamarar zinariya daure a ƙirjinsa.
14 His head, and heares were white as white wooll, and as snowe, and his eyes were as a flame of fire,
Kansa da kuma gashin fari ne fat kamar ulu, fari kamar dusar ƙanƙara, idanunsa kuwa kamar harshen wuta.
15 And his feete like vnto fine brasse, burning as in a fornace: and his voyce as the sounde of many waters.
Sawunsa sun yi kamar tagullar da take haske cikin matoya, muryarsa kuma ta yi kamar muryar ruwaye masu gudu.
16 And he had in his right hand seuen starres: and out of his mouth went a sharpe two edged sword: and his face shone as the sunne shineth in his strength.
A hannunsa na dama ya riƙe taurari bakwai, daga bakinsa kuwa takobi mai kaifi biyu ya fito. Fuskarsa ta yi kamar rana mai haskakawa da dukan haskenta.
17 And when I saw him, I fell at his feete as dead: then he laid his right hand vpon me, saying vnto me, Feare not: I am that first and that last,
Sa’ad da na gan shi, sai na fāɗi a gabansa sai ka ce matacce. Sai ya ɗibiya hannunsa na dama a kaina ya ce, “Kada ka ji tsoro. Ni ne Farko da kuma Ƙarshe.
18 And am aliue, but I was dead: and beholde, I am aliue for euermore, Amen: and I haue the keyes of hell and of death. (aiōn , Hadēs )
Ni ne Rayayye, dā na mutu, ga shi kuwa ina a raye har abada abadin! Ina kuma riƙe da mabuɗan mutuwa da na Hades. (aiōn , Hadēs )
19 Write the things which thou hast seene, and the things which are, and the things which shall come hereafter.
“Saboda haka, ka rubuta abin da ka gani, abin da yake yanzu, da abin da zai faru nan gaba.
20 The misterie of the seuen starres which thou sawest in my right hand, and the seuen golden candlestickes, is this, The seuen starres are the Angels of the seuen Churches: and the seuen candlestickes which thou sawest, are the seuen Churches.
Asirin taurari bakwai da ka gani a hannuna na dama da kuma na alkukan fitilu bakwai na zinariya shi ne, Taurarin bakwai ɗin nan, mala’ikun ikkilisiyoyi bakwai ne; alkukan fitilu bakwai ɗin nan kuma ikkilisiyoyi bakwai ne.