< Luke 18 >

1 And he spake also a parable vnto them, to this ende, that they ought alwayes to pray, and not to waxe faint,
Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
2 Saying, There was a iudge in a certaine citie, which feared not God, neither reuereced man.
Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
3 And there was a widowe in that citie, which came vnto him, saying, Doe mee iustice against mine aduersarie.
A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
4 And hee would not of a long time: but afterward he said with himselfe, Though I feare not God, nor reuerence man,
“An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
5 Yet because this widowe troubleth mee, I will doe her right, lest at the last shee come and make me wearie.
amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
6 And the Lord said, Heare what the vnrighteous iudge saith.
Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
7 Now shall not God auenge his elect, which cry day and night vnto him, yea, though he suffer long for them?
Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
8 I tell you he will auenge them quickly: but when the Sonne of man commeth, shall he finde faith on the earth?
Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
9 He spake also this parable vnto certaine which trusted in themselues that they were iust, and despised other.
Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
10 Two men went vp into the Temple to pray: the one a Pharise, and the other a Publican.
“Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
11 The Pharise stoode and prayed thus with himselfe, O God, I thanke thee that I am not as other men, extortioners, vniust, adulterers, or euen as this Publican.
Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
12 I fast twise in the weeke: I giue tithe of all that euer I possesse.
Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
13 But the Publican standing a farre off, woulde not lift vp so much as his eyes to heauen, but smote his brest, saying, O God, be mercifull to me a sinner.
“Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
14 I tell you, this man departed to his house iustified, rather then the other: for euery man that exalteth himselfe, shall be brought lowe, and he that humbleth himselfe, shalbe exalted.
“Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
15 They brought vnto him also babes that he should touche them. And when his disciples sawe it, they rebuked them.
Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
16 But Iesus called them vnto him, and said, Suffer the babes to come vnto mee, and forbid them not: for of such is the kingdome of God.
Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
17 Verely I say vnto you, whosoeuer receiueth not the kingdome of God as a babe, he shall not enter therein.
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
18 Then a certaine ruler asked him, saying, Good Master, what ought I to doe, to inherite eternall life? (aiōnios g166)
Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
19 And Iesus said vnto him, Why callest thou me good? none is good, saue one, euen God.
Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
20 Thou knowest the comandements, Thou shalt not commit adulterie: Thou shalt not kill: Thou shalt not steale: Thou shalt not beare false witnes: Honour thy father and thy mother.
Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
21 And hee saide, All these haue I kept from my youth.
Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
22 Nowe when Iesus heard that, he saide vnto him, Yet lackest thou one thing. Sell all that euer thou hast, and distribute vnto the poore, and thou shalt haue treasure in heauen, and come follow mee.
Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
23 But when he heard those things, he was very heauie: for he was marueilous riche.
Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
24 And when Iesus sawe him very sorowfull, he said, With what difficultie shall they that haue riches, enter into the kingdome of God!
Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
25 Surely it is easier for a camel to go through a needles eye, then for a riche man to enter into the kingdome of God.
Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
26 Then said they that heard it, And who then can be saued?
Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
27 And he said, The things which are vnpossible with men, are possible with God.
Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
28 Then Peter said, Loe, we haue left all, and haue followed thee.
Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
29 And he said vnto them, Verely I say vnto you, there is no man that hath left house, or parents, or brethren, or wife, or children for the kingdome of Gods sake,
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
30 Which shall not receiue much more in this world, and in the world to come life euerlasting. (aiōn g165, aiōnios g166)
da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Then Iesus tooke vnto him ye twelue, and said vnto them, Beholde, we goe vp to Hierusalem, and all things shalbe fulfilled to the Sonne of man, that are writttn by the Prophets.
Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
32 For he shall be deliuered vnto the Gentiles, and shalbe mocked, and shalbe spitefully entreated, and shalbe spitted on.
Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
33 And when they haue scourged him, they will put him to death: but the thirde day hee shall rise againe.
za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
34 But they vnderstood none of these things, and this saying was hidde from them, neither perceiued they the things, which were spoken.
Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
35 And it came to passe, that as he was come neere vnto Iericho, a certaine blinde man sate by the way side, begging.
Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
36 And when he heard the people passe by, he asked what it meant.
Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
37 And they saide vnto him, that Iesus of Nazareth passed by.
Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
38 Then hee cried, saying, Iesus the Sonne of Dauid, haue mercie on me.
Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
39 And they which went before, rebuked him that he shoulde holde his peace, but he cried much more, O Sone of Dauid, haue mercie on me.
Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
40 And Iesus stoode stil, and commanded him to be brought vnto him. And when he was come neere, he asked him,
Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
41 Saying, What wilt thou that I doe vnto thee? And he said, Lord, that I may receiue my sight.
“Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
42 And Iesus said vnto him, Receiue thy sight: thy faith hath saued thee.
Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
43 Then immediatly he receiued his sight, and followed him, praysing God: and all the people, when they sawe this, gaue praise to God.
Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.

< Luke 18 >