< 2 Corinthians 1 >
1 Pavl an Apostle of JESVS Christ, by the will of God, and our brother Timotheus, to the Church of God, which is at Corinthus with all the Saints, which are in all Achaia:
Bulus, manzon Kiristi Yesu ta wurin nufin Allah, da kuma daga Timoti ɗan’uwanmu, Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, tare da dukan tsarkaka a ko’ina a Akayya.
2 Grace be with you, and peace from God our Father, and from the Lord Iesus Christ.
Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
3 Blessed be God, euen the Father of our Lord Iesus Christ, the Father of mercies, and the God of all comfort,
Yabo ya tabbata ga Allah, da Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba mai tausayi, da kuma Allah na dukan ta’aziyya,
4 Which comforteth vs in all our tribulation, that we may be able to comfort them which are in any affliction by the comfort wherewith we our selues are comforted of God.
wanda yakan yi mana ta’aziyya a cikin dukan wahalolinmu, domin mu kuma mu iya ta’azantar da waɗanda suke cikin kowace irin wahala, da ta’aziyyar da mu kanmu muka samu daga Allah.
5 For as the sufferings of Christ abounde in vs, so our consolation aboundeth through Christ.
Gama kamar yadda wahalar Kiristi ta cika har tana zuba a cikin rayuwarmu, haka nan kuma ta wurin Kiristi ta’aziyyarmu ta cika har tana zuba.
6 And whether we be afflicted, it is for your consolation and saluation, which is wrought in the induring of the same sufferings, which we also suffer: or whether we be comforted, it is for your consolation and saluation.
In muna shan wahala, ai, muna shanta domin ta’aziyyarku, da cetonku ne, in mun sami ta’aziyya, ai, mun same ta domin ta’aziyyarku ce, wadda take sa ku jure wa irin wahalan nan, da muke sha.
7 And our hope is stedfast concerning you, in as much as we know that as ye are partakers of the sufferings, so shall ye be also of the consolation.
Begen da muke da shi dominku kuwa, tabbatacce ne, domin mun san cewa kamar yadda kuke tarayya da mu a cikin wahalolinmu, haka kuma kuke tarayya da mu a cikin ta’aziyyarmu.
8 For brethren, we woulde not haue you ignorant of our affliction, which came vnto vs in Asia, howe we were pressed out of measure passing strength, so that we altogether doubted, euen of life.
’Yan’uwa, ba ma so ku zama da rashin sani, a kan wahalolin da muka sha a lardin Asiya. Mun sha wahaloli sosai, har abin ya fi ƙarfinmu, ya sa muka fid da tsammanin rayuwa.
9 Yea, we receiued the sentence of death in our selues, because we shoulde not trust in our selues, but in God, which rayseth the dead.
Ba shakka, a zuciyarmu mun ji kamar hukuncin kisa ne aka yi mana. Wannan kuwa ya faru ne domin kada mu dogara da kanmu, sai dai ga Allah, wanda yake tā da matattu.
10 Who deliuered vs from so great a death, and doeth deliuer vs: in whom we trust, that yet hereafter he will deliuer vs,
Shi ya cece mu daga irin wannan hatsari na mutuwa, zai kuwa cece mu. A kansa muka kafa bege cewa zai ci gaba da cetonmu,
11 So that ye labour together in prayer for vs, that for the gift bestowed vpon vs for many, thankes may be giuen by many persons for vs.
yayinda kuke taimakonmu ta wurin addu’o’inku. Mutane da yawa kuwa za su yi godiya ta dalilinmu, saboda albarkar da aka yi mana, ta amsa addu’o’i masu yawa.
12 For our reioycing is this, the testimonie of our conscience, that in simplicitie and godly purenesse, and not in fleshly wisedome, but by the grace of God wee haue had our conuersation in the worlde, and most of all to you wardes.
Wannan shi ne taƙamarmu. Lamirinmu yana ba da shaida cewa mun yi zamanmu a duniya, musamman a dangantakarmu da ku cikin tsarki, tsakani da Allah. Mun yi haka ta wurin bishewar alherin Allah, ba bisa ga hikimar duniya ba.
13 For wee write none other thinges vnto you, then that ye reade or els that ye acknowledge, and I trust ye shall acknowledge vnto ye end.
Gama ba mu rubuta muku abin da ba za ku iya karatu ko ku kāsa fahimta ba. Ina kuma fata cewa,
14 Euen as ye haue acknowledged vs partly, that we are your reioycing, euen as ye are ours, in the day of our Lord Iesus.
kamar yadda kuka ɗan fahimce mu, za ku kai ga cikakkiyar fahimta cewa za ku iya yin taƙama da mu, kamar yadda mu ma za mu yi taƙama da ku a ranar da Ubangiji Yesu zai dawo.
15 And in this confidence was I minded first to come vnto you, that ye might haue had a double grace,
Saboda na amince da haka, shi ya sa na so zuwa wurinku da fari, domin ku sami albarka riɓi biyu.
16 And to passe by you into Macedonia, and to come againe out of Macedonia vnto you, and to be led foorth towarde Iudea of you.
Na yi shiri in ziyarce ku a kan hanyata zuwa Makidoniya, in kuma sāke dawo wurinku a kan hanyata daga Makidoniya, sa’an nan ku yi mini rakiya a hanyata zuwa Yahudiya.
17 When I therefore was thus minded, did I vse lightnesse? or minde I those thinges which I minde, according to the flesh, that with me should be, Yea, yea, and Nay, nay?
Kuna gani na yi wannan shirin ba da sanin abin da nake yi ba ne? Ko kuwa, kuna gani na yi shirin nan da halin mutuntaka ne, don in ce, “I” in koma in ce, “A’a”?
18 Yea, God is faithfull, that our worde towarde you was not Yea, and Nay.
Kamar dai yadda ba shakka Allah yake mai aminci, haka ma maganar da muka yi muku, ba “I” da kuma “A’a” ba ce.
19 For the Sonne of God Iesus Christ, who was preached among you by vs, that is, by me, and Siluanus, and Timotheus, was not Yea, and Nay: but in him it was Yea.
Gama Ɗan Allah, Yesu Kiristi, wanda ni da Sila da Timoti muka yi muku wa’azinsa, ai, ba “I” da “A’a” ba ne, amma a cikin Kiristi, “I” ne kullum.
20 For all the promises of God in him are Yea, and are in him Amen, vnto the glorie of God through vs.
Domin dukan alkawaran Allah cikarsu a gare shi suke, ta wurinsa ne kuma muke faɗar “Amin”, domin a ɗaukaka Allah.
21 And it is God which stablisheth vs with you in Christ, and hath anoynted vs.
Allah ne fa yake sa mu da ku mu tsaya daram cikin Kiristi. Shi ne ya shafe mu,
22 Who hath also sealed vs, and hath giuen the earnest of the Spirit in our hearts.
ya buga mana hatiminsa a kan mu nasa ne, ya kuma sa mana Ruhunsa a cikin zukatanmu, domin yă tabbatar da abin da yake zuwa nan gaba.
23 Nowe, I call God for a recorde vnto my soule, that to spare you, I came not as yet vnto Corinthus.
Labudda, Allah shi ne shaidata cewa don kada in ƙara muku wahala ne ya sa ban koma Korint ba.
24 Not that wee haue dominion ouer your faith, but wee are helpers of your ioy: for by faith yee stande.
Ba nuna muku iko a kan bangaskiyarku muke yi ba, sai dai muna aiki tare da ku ne saboda farin cikinku, domin bisa ga bangaskiya ce kuke tsaye da ƙarfi.