< 1 Corinthians 11 >

1 Be yee followers of mee, euen as I am of Christ.
Ku bi gurbina, kamar yadda ni nake bin gurbin Kiristi.
2 Now brethren, I commend you, that ye remember all my things, and keepe the ordinances, as I deliuered them to you.
Ina yabonku saboda kuna tunawa da ni a cikin kowane abu, kuna kuma riƙe da koyarwar, yadda na ba ku.
3 But I wil that ye know, that Christ is the head of euery man: and the man is the womans head: and God is Christs head.
To, ina so ku gane cewa shugaban kowane namiji Kiristi ne, shugaban mace namiji ne, shugaban Kiristi kuma Allah ne.
4 Euery man praying or prophecying hauing any thing on his head, dishonoureth his head.
Kowane namijin da ya yi addu’a ko annabci da kansa a rufe ya jawo kunya wa kansa.
5 But euery woman that prayeth or prophecieth bare headed, dishonoureth her head: for it is euen one very thing, as though she were shauen.
Duk macen da ta yi addu’a ko annabci da kanta a buɗe kuwa ta rena kanta, ya zama kamar an aske kanta ke nan.
6 Therefore if the woman be not couered, let her also be shorne: and if it be shame for a woman to be shorne or shauen, let her be couered.
In mace ba ta so tă rufe kanta, to, sai tă aske gashinta; in kuwa abin kunya ne mace tă yanke ko tă aske gashinta, to, sai tă rufe kanta.
7 For a man ought not to couer his head: for as much as he is the image and glory of God: but the woman is the glory of the man.
Namiji kuwa bai kamata ya rufe kansa ba, da yake shi kamannin Allah ne, da kuma darajar Allah, amma mace dai, darajar namiji ne.
8 For the man is not of the woman, but the woman of the man.
Gama namiji bai fito daga mace ba, sai dai mace ce ta fito daga namiji.
9 For the man was not created for the womans sake: but the woman for the mans sake.
Ba a kuma halicci namiji don mace ba, sai dai mace don namiji.
10 Therefore ought the woman to haue power on her head, because of the Angels.
Don haka, saboda wannan, da kuma saboda mala’iku, dole mace ta ɗaura wani abu a kanta.
11 Neuertheles, neither is the man without the woman, neither the woman without the man in the Lord.
Duk da haka a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, namiji kuma ba a rabe yake da mace ba.
12 For as the woman is of the man, so is the man also by the woman: but all things are of God.
Kamar yadda mace ta fito daga namiji, haka kuma aka haifi namiji ta wurin mace. Sai dai kowane abu daga Allah yake.
13 Iudge in your selues, Is it comely that a woman pray vnto God vncouered?
Ku kanku duba mana. Ya yi kyau mace tă yi addu’a ga Allah da kanta a buɗe?
14 Doeth not nature it selfe teach you, that if a man haue long heare, it is a shame vnto him?
Kai, yadda halitta take ma, ai, ta koya muku cewa in namiji yana da dogon gashi, abin kunya ne a gare shi,
15 But if a woman haue long heare, it is a prayse vnto her: for her heare is giuen her for a couering.
amma in mace tana da dogon gashi, ai, daraja ce a gare ta. Gama an ba ta dogon gashi saboda rufe kanta ne.
16 But if any man lust to be contentious, we haue no such custome, neither the Churches of God.
In akwai mai gardama da wannan, to, mu dai ba mu da wata al’ada, haka ma ikkilisiyoyin Allah.
17 Nowe in this that I declare, I prayse you not, that ye come together, not with profite, but with hurt.
Game da umarnan nan dai, ban yaba muku ba, domin taruwarku ba ta kirki ba ce, ɓarna ce.
18 For first of all, when ye come together in the Church, I heare that there are dissentions among you: and I beleeue it to be true in some part.
Da farko dai, na ji cewa sa’ad da kuka taru a matsayin ikkilisiya, akwai tsattsaguwa a tsakaninku, har na fara yarda da zancen.
19 For there must be heresies euen among you, that they which are approoued among you, might be knowen.
Ba shakka dole a sami bambanci a tsakaninku don a nuna wa Allah ya amince da shi a cikinku.
20 When ye come together therefore into one place, this is not to eate the Lords Supper.
Sa’ad da kuka taru, ba Cimar Ubangiji kuke ci ba,
21 For euery man when they should eate, taketh his owne supper afore, and one is hungry, and another is drunken.
gama yayinda kuke ci, kowa yakan ci gaba ba tare da jiran wani ba. Wani yă zauna da yunwa, wani kuma yă bugu.
22 Haue ye not houses to eate and to drinke in? despise ye the Church of God, and shame them that haue not? what shall I say to you? shall I prayse you in this? I prayse you not.
Kai, ba ku da gidajen da za ku ci ku sha ne? Ko dai kun rena ikkilisiyar Allah ne, kuna kuma wulaƙanta waɗanda ba su da kome? Me zan ce muku? In yabe ku ne game da wannan? A’a, ko kaɗan!
23 For I haue receiued of the Lord that which I also haue deliuered vnto you, to wit, That the Lord Iesus in the night when he was betrayed, tooke bread:
Gama abin da na karɓa daga wurin Ubangiji shi ne nake ba ku. Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi, ya ɗauki burodi,
24 And when hee had giuen thankes, hee brake it, and sayde, Take, eate: this is my body, which is broken for you: this doe ye in remembrance of me.
bayan ya yi godiya, sai ya kakkarya ya ce, “Wannan jikina ne, wanda yake dominku, ku yi wannan don tunawa da ni.”
25 After the same maner also he tooke the cup, when he had supped, saying, This cup is the Newe Testament in my blood: this doe as oft as ye drinke it, in remembrance of me.
Haka kuma bayan cimar, ya ɗauki kwaf, yana cewa, “Wannan kwaf ne sabon alkawari a jinina; ku yi wannan, a duk sa’ad da kuke sha, don tunawa da ni.”
26 For as often as ye shall eate this bread, and drinke this cup, ye shewe the Lords death till hee come.
Gama a duk sa’ad da kuke cin wannan burodi, kuke kuma sha daga wannan kwaf, kuna shelar mutuwar Ubangiji ne har yă dawo.
27 Wherefore, whosoeuer shall eate this bread, and drinke the cup of the Lord vnworthily, shall be guiltie of the body and blood of the Lord.
Saboda haka, duk wanda ya ci burodin ko ya sha daga kwaf na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulaƙanta jiki da jinin Ubangiji ke nan.
28 Let euery man therefore examine himselfe, and so let him eate of this bread, and drinke of this cup.
Dole kowa yă bincike kansa kafin yă ci burodin yă kuma sha daga kwaf ɗin.
29 For he that eateth and drinketh vnworthily, eateth and drinketh his owne damnation, because he discerneth not the Lords body.
Gama duk wanda ya ci ya kuma sha ba tare da fahimtar jikin Ubangiji ba, ya ci ya kuma sha wa kansa hukunci ne.
30 For this cause many are weake, and sicke among you, and many sleepe.
Shi ya sa da yawa a cikinku ba su da ƙarfi, suna kuma da rashin lafiya, waɗansunku kuma sun riga sun yi barci.
31 For if we would iudge our selues, we should not be iudged.
Amma in da za mu auna kanmu sosai, da ba za mu shiga irin hukuncin nan ba.
32 But when we are iudged, we are chastened of the Lord, because we should not be condemned with the world.
Duk da haka sa’ad da Ubangiji ya hukunta mu, ana yin mana horo ne don kada a ƙarshe a hallaka mu tare da duniya.
33 Wherefore, my brethren, when ye come together to eate, tary one for another.
Saboda haka’yan’uwana, sa’ad da kuka taru don ci, ku jira juna.
34 And if any man be hungry, let him eate at home, that ye come not together vnto condemnation. Other things will I set in order when I come.
In wani yana jin yunwa, sai yă ci abinci a gida, saboda in kuka taru kada yă jawo hukunci. Sa’ad da na zo kuma zan ba da ƙarin umarnai.

< 1 Corinthians 11 >