< Izaiáš 13 >

1 Břímě Babylona, kteréž viděl Izaiáš syn Amosův.
Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.
2 Na hoře vysoké vyzdvihněte korouhev, povyšte hlasu k nim, dejte návěští rukou, ať vejdou do bran knížecích.
A tā da tuta a kan tudun da yake mai fili, ka tā da murya gare su; ka ɗaga hannu ka ba su alama don su shiga ƙofofi masu alfarma.
3 Já jsem přikázal posvěceným svým, povolal jsem také i udatných reků svých k vykonání hněvu svého, veselících se z vyvýšení mého.
Na umarci tsarkakana; na umarci jarumawan yaƙina su gamsar da fushina, waɗanda suke farin ciki a nasarata.
4 Hlas množství na horách, jakožto lidu mnohého, hlas a zvuk království a národů shromážděných: Hospodin zástupů sbírá vojsko k válce.
Ka saurara, akwai surutu a kan duwatsu, sai ka ce na babban taron jama’a! Ka saurara, akwai hayaniya a cikin mulkoki, sai ka ce al’ummai ne suna ta tattaruwa! Ubangiji Maɗaukaki yana shirya mayaƙa don yaƙi.
5 Táhnou z země daleké od končin nebes. Hospodin a osudí prchlivosti jeho, aby poplénil všecku zemi.
Suna zuwa daga ƙasashe masu nesa, daga iyakokin duniya, Ubangiji da kuma fushinsa, zai hallaka dukan ƙasar.
6 Kvělte, nebo blízko jest den Hospodinův, jako zpuštění od Všemohoucího přijde.
Ku yi ihu, gama ranar Ubangiji ta yi kusa za tă zo kamar hallaka daga Maɗaukaki.
7 A protož všeliké ruce oslábnou, a všeliké srdce člověka rozplyne se.
Saboda wannan, hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.
8 I budou předěšeni, svírání a bolesti je zachvátí, jako rodička stonati budou; každý nad bližním svým užasne se, tváře jejich k plameni podobné budou.
Tsoro zai kama su, zafi da azaba za su ci ƙarfinsu; za su yi ta murɗewa kamar mace mai naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu a ɓace.
9 Aj, den Hospodinův přichází přísný, a zůřivost a rozpálení hněvu, aby obrátil tu zemi v poušť, a hříšníky její z ní vyhladil.
Duba, ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana, mai hasala da zafin fushi, don ta mai da ƙasar kango ta kuma hallakar da masu zunubi da suke cikinta.
10 Nebo hvězdy nebeské a planéty jejich nedopustí svítiti světlu svému; zatmí se slunce při vycházení svém, a měsíc nevydá světla svého.
Taurarin sama da ƙungiyoyinsu ba za su ba da haskensu ba. Rana za tă yi duhu wata kuma ba zai ba da haskensa ba.
11 A navštívím na okršlku země zlost, a na bezbožných nepravost jejich; a káži přestati pýše pyšných, a vysokomyslnost tyranů snížím.
Zan hukunta duniya saboda muguntarta, mugaye saboda zunubansu. Zan kawo ƙarshe ga girman kan masu taƙama in kuma ƙasƙantar da ɗaga kan marasa tausayi.
12 Způsobím to, že dražší bude člověk nad zlato čisté, člověk, pravím, nad zlato z Ofir.
Zan sa mutum yă fi zinariya zalla wuyar samuwa, fiye da zinariyar Ofir wuyan gani.
13 Z té příčiny zatřesu nebesy, a pohne se země z místa svého, v prchlivosti Hospodina zástupů, a ve dni rozpálení hněvu jeho.
Saboda haka zan sa sammai su yi rawar jiki; duniya kuma za tă girgiza daga inda take a fushin Ubangiji Maɗaukaki, a ranar fushinsa mai ƙuna.
14 I bude jako srna zplašená, a jako stádo, když není, kdo by je shromáždil; jeden každý k lidu svému se obrátí, a každý do země své uteče.
Kamar barewar da ake farautarta kamar tumaki marasa makiyayi, haka nan kowane mutum zai koma ga mutanensa, kowane mutum zai gudu zuwa ƙasarsa.
15 Kdožkoli nalezen bude, bude proboden, a kteříž by se koli shlukli, od meče padnou.
Duk wanda aka kama za a soke shi yă mutu; dukan waɗanda aka kama za su mutu ta takobi.
16 Nadto i dítky jejich rozrážíny budou před očima jejich, domové jejich zloupeni, a ženy jejich poškvrněny.
Za a fyaɗa’ya’yansu a ƙasa su yi kucu-kucu a idanunsu; za a washe gidajensu, a kuma kwana da matansu.
17 Aj, já vzbudím proti nim Médské, kteříž sobě stříbra nebudou vážiti, a v zlatě nebudou se kochati,
Duba, zan zuga mutanen Medes su yi gāba da su, su da ba su kula da azurfa ba kuma ba sa damuwa da zinariya.
18 Ale z luků dítky rozrážeti, aniž se nad plodem života slitují, aniž synům odpustí oko jejich.
Bakkunansu za su kashe samari; ba za su ji tausayin jarirai ba ba za su kuwa nuna jinƙai ga’yan yara ba.
19 I budeť Babylon, někdy ozdoba království a okrasa důstojnosti Kaldejské, podobný podvrácené Sodomě a Gomoře.
Babilon, kayan daraja na mulkoki, abin fariyar Babiloniyawa, Allah zai kaɓantar da ita kamar yadda ya yi da Sodom da Gomorra.
20 Nebudou se v něm osazovati na věky, ani bydliti od pokolení až do pokolení; aniž rozbije tam stanu svého Arab, ani pastýři tam odpočívati budou.
Ba za ƙara kasance da mazauna kuma ba ko a yi zama a cikinta dukan zamanai; Ba wani mutumin Arab da zai kafa tentinsa a can, ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.
21 Ale lítá zvěř tam odpočívati bude, a domové jejich šelmami naplněni budou; bydliti budou tam i sovy, a příšery tam skákati budou.
Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.
22 Ozývati se také budou sobě hrozné potvory na palácích jejich, a draci na hradích rozkošných. A blízkoť jest, že přijde čas jeho, a dnové jeho prodlévati nebudou.
Kuraye za su yi ta kuka a kagarorinta, diloli kuma a cikin fadodinta masu alfarma. Lokacinta ya yi kusa, kwanakinta kuma ba za su yi tsawo ba.

< Izaiáš 13 >