< Římanům 11 >

1 Protož pravím: Zdaliž Bůh zavrhl lid svůj? Nikoli; nebo i já Izraelský jsem, z semene Abrahamova, z pokolení Beniaminova.
Sai na ce, Allah ya ki mutanensa ne? Ba zai taba yiwuwa ba. Domin ni ma ba-Isra'ile ne, na zuriyar Ibrahim, a kabilar Bilyaminu.
2 Nezavrhlť Bůh lidu svého, kterýž předzvěděl. Zdali nevíte, co písmo praví o Eliášovi, kterak se modlí Bohu proti lidu Izraelskému, řka:
Allah bai ki mutanen sa da ya ke da rigyasaninsu ba. Ko kun san abin da nassi ya ce game da Iliya, yadda ya kai karar Isra'ila a gaban Allah?
3 Pane, proroky tvé zmordovali, a oltáře tvé rozkopali, já pak zůstal jsem sám, a i méť duše hledají?
Ya ce, ''Ubangiji, sun kashe annabawanka, sun rushe alfarwanka kuma, Ni kadai ne na rage, ga shi suna neman su kashe ni.''
4 Ale co jemu dí odpověď Boží? Pozůstavil jsem sobě sedm tisíců mužů, kteříž neskláněli kolen před Bálem.
Amma wacce amsa ce Allah ya ba shi? Ya ce, ''Ina da mutane dubu bakwai da na kebe don kaina, da ba su taba rusuna wa Ba'al ba.''
5 Takť i nyní ostatkové podlé vyvolení milosti zůstali,
Ban da haka ma, ban da haka ma a wannan lokacin akwai sauran zabe na alheri.
6 A poněvadž z milosti, tedy ne z skutků, sic jinak milost již by nebyla milost. Pakli z skutků, již není milost, jinak skutek nebyl by skutek.
Amma tun da ta wurin alheri ne, ba ga ayyuka ba. In ba haka ba, alheri ba zai zama alheri ba kenan.
7 Což tedy? Čeho hledá Izrael, toho nedošel, ale vyvolení došli toho, jiní pak zatvrzeni jsou,
Sai kuma me? Abin da Isra'ila ke nema, ba su samu ba, amma zababbun sun same shi, saura kuma sun taurare.
8 (Jakož psáno jest: Dal jim Bůh ducha zkormoucení, oči aby neviděli, a uši, aby neslyšeli, ) až do dnešního dne.
Kamar yadda yake a rubuce, ''Allah ya ba su ruhun rashin fahimta, ga idanu amma ba za su gani ba, ga kunnuwa amma ba za su ji ba, har zuwa wannan rana.''
9 A David dí: Budiž jim stůl jejich osídlem a pastmi a pohoršením i odplacením.
Dauda kuma ya ce, ''bari teburinsu ya zama taru, da tarko, ya zama dutsen tuntube da abin ramako a gare su.
10 Zatmětež se oči jejich, ať nevidí, a hřbet jejich vždycky shýbej.
Bari idanunsu ya duhunta domin kada su gani; bayansu kuma a duke kullum.''
11 Pravím tedy: Tak-liž pak klesli, aby padli? Nikoli, ale jejich pádem spasení přišlo pohanům, aby je k závidění přivedl.
Na ce, ''sun yi tuntube domin su fadi ne?'' Kada abu kamar haka ya faru. A maimakon haka, juyawa baya da suka yi ya sa, ceto ya zo ga Al'ummai, domin ya sa su kishi.
12 A poněvadž pak jejich pád jest bohatství světa, a zmenšení jejich jest bohatství pohanů, čím více plnost jich?
Idan yanzu juyawa baya da sun yi ya zama arziki ga duniya, rashin su kuma arziki ga Al'ummai, yaya kwatancin girmansa zai kasance in sun zo ga kammala?
13 Vámť zajisté pravím pohanům, že jelikož jsem já apoštol pohanský, přisluhování své oslavuji,
Yanzu ina magana da ku ku da ke Al'ummai. Tunda yake ni ne manzo ga Al'ummai, ina kuma fahariya cikin hidimata.
14 Zda bych jak k závidění vzbuditi mohl tělo mé, a k spasení přivesti některé z nich.
Yana yiwuwa in sa ''yan'uwa na kishi, domin mu ceci wadansu su.
15 Nebo kdyžť zavržení jich jest smíření světa, co pak zase jich přijetí, než život z mrtvých?
Idan kinsu ya kawo sulhuntawa ga duniya, Karbarsu kuma zata zama yaya? Zata zama rai ne daga mutuwa.
16 Poněvadž prvotiny svaté, takéť i těsto; a jestliť kořen svatý, i ratolesti.
'ya'yan farko sunan haka ma kakkabensu yake, Idan saiwar itace na nan, haka ma rassan za su zama.
17 Žeť jsou pak některé ratolesti vylomeny, a ty, byv planou olivou, vštípen jsi místo nich, a učiněn jsi účastník kořene i tučnosti olivy.
Amma idan an karye wasu daga cikin rassan, idan ku rassan zaitun na ainihi ne, da aka samu daga cinkinsu, kuma idan kuna da gado tare da su, acikin saiwar itacen zaitun din.
18 Nechlub se proti ratolestem. Pakli se chlubíš, věz, že ne ty kořen neseš, ale kořen tebe.
Kada ku yi fahariya a kan rassan. Amma idan kuka yi fahariya to ba ku bane masu karfafa saiwar amma saiwar ce ke karfafa ku.
19 Pakli díš: Vylomeny jsou ratolesti, abych já byl vštípen,
Kana iya cewa, ''An karye rassan domin a same ni a ciki.''
20 Dobře. Pro nevěru vylomeny jsou, ale ty věrou stojíš. Nebudiž vysokomyslný, ale boj se.
Wannan gaskiya ne! Saboda rashin bangaskiyarsu ne ya sa aka karye su daga rassan, amma ku tsaya da karfi acikin bangaskiyarku. Kada ku dauki kanku fiye da yadda ya kamata, amma ku ji tsoro.
21 Nebo poněvadž Bůh ratolestem přirozeným neodpustil, věz, žeť by ani tobě neodpustil.
Domin idan Allah bai bar ainihin rassan ba, to ba zai bar ku ba.
22 A protož viz dobrotivost i zůřivost Boží. K těm zajisté, kteříž padli, zůřivost, ale k tobě dobrotivost, ač budeš-li trvati v dobrotě. Sic jinak i ty vyťat budeš.
Ku duba yadda irin ayyuka masu tsananni na Allah. Ta daya hannun kuma, tsanannin kan zoa kan Yahudawa wadanda suka fadi. Har 'ila yau jinkai Allah ya zo maku, idan kun cigaba cikin alherinsa baza a sare ku ba. Amma in kun ki za a sare ku.
23 Ano i oni, jestliže nezůstanou v nevěře, zase vštípeni budou. Mocenť jest zajisté Bůh zase vštípiti je.
Hakanan, idan ba su ci gaba cikin rashin bangaskiyarsu ba, za a maida su cikin itacen. Domin Allah zai iya sake maida su.
24 Nebo poněvadž ty vyťat jsi z přirozené plané olivy, a proti přirození vštípen jsi v dobrou olivu, čím více ti, kteříž podlé přirození jsou, vštípeni budou v svou vlastní olivu.
Idan an yanke ka daga itacen zaitun da ke na jeji, har ya yiwu an hada ka cikin itacen zaitun na ainihi, yaya kuma wadannan Yahudawa wadanda sune ainihin rassan, da za'a maido cikin zaitun da ke na ainihi?
25 Neboť nechci, bratří, abyste nevěděli tohoto tajemství, (abyste nebyli sami u sebe moudří, ) že zatvrdilost z částky přihodila se Izraelovi, dokudž by nevešla plnost pohanů.
Yan'uwa, ba na so ku kasance cikin duhu a game da wannan asirin, domin kada ku zama da hikima cikin tunaninku. Wannan asirin shine cewa wannan taurarewa ta faru a Isra'ila, har sai da Al'ummai suka shigo ciki.
26 A takť všecken Izrael spasen bude, jakož psáno jest: Přijde z Siona vysvoboditel, a odvrátíť bezbožnosti od Jákoba.
Ta haka dukan Isra'ila za su tsira, kamar yadda yake a rubuce: ''Daga cikin Sihiyona mai Kubutarwa zai fito; Zai kawar da kazanta daga cikin Yakubu.
27 A tatoť bude smlouva má s nimi, když shladím hříchy jejich.
Wannan zai zama alkawarina da su, sa'adda na kawar da zunubansu.''
28 A tak s strany evangelium jsouť nepřátelé pro vás, ale podlé vyvolení jsou milí pro otce.
A wani bangaren kuma game da bishara, su makiya ne amamadinku, ta wani fannin kuma bisa ga zabin Allah su kaunattatu ne saboda ubanni.
29 Darů zajisté svých a povolání Bůh nelituje.
Domin baye-baye da kiran Allah basa canzawa.
30 Nebo jakož i vy někdy jste nebyli poslušni Boha, ale nyní milosrdenství jste došli pro jejich nevěru,
Domin ku ma da ba ku yin biyayya ga Allah, amma yanzu kun sami jinkai saboda rashin biyayyarsu.
31 Tak i oni nyní neuposlechli, aby pro učiněné vám milosrdenství i oni milosrdenství dosáhli.
Ta wannan hanyar dai, wadannan Yahudawan sun zama marasa biyayya. Sakamakon haka shine ta wurin jinkan da aka nuna maku, suma su samu jikai yanzu.
32 Zavřel zajisté Bůh všecky v nevěře, aby se nade všemi smiloval. (eleēsē g1653)
Domin Allah ya rufe kowa ga rashin biyayya, domin ya nuna jinkai ga kowa. (eleēsē g1653)
33 Ó hlubokosti bohatství i moudrosti i umění Božího! Jak jsou nezpytatelní soudové jeho, a nevystižitelné cesty jeho.
Ina misalin zurfin wadata da kuma hikima da sani na Allah! Hukunce-hukuncensa sun fi gaban a bincika, hanyoyinsa kuma sun fi gaban ganewa!
34 Nebo kdo poznal mysl Páně? Aneb kdo jemu radil?
Don wanene ya san tunanin Ubangiji? Wanene kuma ya zama mai bashi shawara?
35 Nebo kdo prvé dal jemu, a budeť mu odplaceno?
Ko kuma, wanene ya fara ba Allah wani abu, domin a biya shi?''
36 Nebo z něho, a skrze něho, a v něm jsou všecky věci, jemuž sláva na věky. Amen. (aiōn g165)
Daga wurinsa ne, ta wurinsa ne kuma, a gare shi ne kuma dukan abu suka fito. A gare shi daukaka ta tabbata har abada. Amin. (aiōn g165)

< Římanům 11 >